• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Friday, March 31, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home General Stories

Shin ta yaya kirarin Kano na “Kano Jalla babbar Hausa” ya gurbace?

August 28, 2022
in General Stories
0
Shin ta yaya kirarin Kano na “Kano Jalla babbar Hausa” ya gurbace?
0
SHARES
13
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga Jaafar Jaafar

Akwai wasu Larabawa da su ka taho shekaru aru-aru daga Makka su ka yada zango, kuma daga bisani su ka kafa gari, har su ka yi kaka-gida a yankin Bargazal (Bahr Ghazal) da ke Sudan.

Mutanen su na da arziki kwarai, saboda cinikin bayi da fatauci. Ana kiran wadannan Larabawa da Jallaba. Daga bisani sunan matsugunninsu ma ya koma Jallaba. Wannan yanki na Kasar Sudan yana da kamanceceniya da Kano saboda arzikinsa da hadahadar cinikin bayi da fatauci da yaki dss.

Sai dai da zanta da Kachallan Kano maigirma Malam Magaji Galadima ta waya dazu, ya ƙara min haske a kan makalar.

Kachalla ya ce min kirarin ya samu gurbacewa ne a dalilin kuskuren ɗab’i da aka yi a labarin “An Ki Cin Biri An Ci Dila” da ke cikin littafin “Magana Jari Ce” na Abubakar Imam. Wannan kuskure na dab’i an yi shi a wannan babi a cikin zantawar Dan’iya da Daudu, wasu shaƙiyyan birni dake sane da yankan aljihu a kasuwar Kurmi, anan ne aka rubuta kirarin ba daidai ba, maimakon a rubuta Jallabar Hausa, sai aka rubuta Jalla babbar Hausa.

A cewar Kachallan Kano, tahirihin wadannan mutanen Jallaba da na kawo haka yake. Sai dai ba kamanceceniyar Jallabar Sudan da Kano ta fannin cinikin bayi da kasuwanci da yaki ne ya sa ake yi wa Kano kirari da “Kano Jallabar Hausa” ba.

Ya ce akwai riga da su ire iren waɗannan Larabawa ke sakawa wadda ita ma a ke kiranta da “Jallaba”. Baƙaken Larabawa dake zaune a Kano kamar Usman Jallaba, ainihi Usman mai Jallaba ake kiransa daga baya ake taƙaitawa ya koma Usman Jallaba. Akwai sauran irinsu Sarkin Fada Zimit da Musa Gashash da su Matawalle Malam Munir duk ita suke sakawa. Ita wannan riga kamar cikar ado ce, domin sai an cancada ado sannan kuma a dora ta a sama kamar alkyabba. Jallaba na kama da alkyabba, ita ma gabanta a bude ya ke. Jallaba na da igiyar ƙullewa guda uku, da wajen zura hannaye kuma ba ta da kokuwa (hood).

A cewar Kachalla, kalmar Hausa da aka yi amfani da ita a wannan kirari ana nufin Sakkwato ko kuma daular Usmaniyya. Bisa ga kasaitar Kano a matsayin garin da ya fi girma da shuhura da arziki a kasar Hausa, shi ya sa ake yi mata kirari da “Jallabar Hausa”, wato cikar kwalliyar kasar Hausa.

Kachallan na Kano har ila yau yace Jalla babbar Hausa bai bada wata ma’ana ingattacciya ba in aka sheƙe aka tankaɗe kalmomin. Ya ƙara da cewa hatta maigirma marigayi Ɗanmasanin Kano a jawabansa Jallabar Hausa ya ke cewa ba Jalla babbar Hausa ba.

ranarhausa2022

Share

Related

Source: Daily Nigerian Hausa
Via: Zaharadeen Mziag
Previous Post

HALIN TSARO KATSINA NA TSAKA MAI WUYA……ZAMFARA CE MATSALARMU

Next Post

Atiku ya sauka a Kano domin karɓar Shekarau zuwa PDP

Next Post
Atiku ya sauka a Kano domin karɓar Shekarau zuwa PDP

Atiku ya sauka a Kano domin karɓar Shekarau zuwa PDP

Recent Posts

  • On birthday, clerics pray for Tinubu, Nigeria in Abuja
  • Gwamna Masari ya Kaddamar da Kwamitin Miƙa Mulki ga sabuwar Gwamnati
  • Masari: Tinubu Na Bukatar Addu’a
  • Bashin Da Ake Bin Najeriya Ya Karu Zuwa N46.25tr —DMO
  • FEC Approves N59.78bn For Ogoni Cleanup Projects

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In