• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Thursday, March 30, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home General Stories

HALIN TSARO KATSINA NA TSAKA MAI WUYA……ZAMFARA CE MATSALARMU

August 28, 2022
in General Stories
0
‘Yan Ta’addar da suka addabi hanyoyin Jibiya da Batsari. ….Sunayen su,Asalinsu,yawansu.
0
SHARES
40
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Sharhin Katsina City News

Jihar Katsina na daya daga cikin yankin da ke tsaka mai wuya a mummunan halin tsaro daga ‘yan bindiga masu kisa da satar mutane a Arewa maso Yamma da kuma kasar nan.

Jihar Zamfara, wadda ita ce kanwa uwar gamin matsalar tsaron ‘yan bindiga da sunan sulhuntawa saboda zaben 2023 da wadannan ‘yan bindigar.

Mafi yawan yarjejeniyar tana kamawa ne kamar haka. Ku kyale dajin Zamfara da mutanenta, amma duk inda kuka je ba ruwanmu.

Daga wannan yarjejeniyar da Zamfara ke yi da ‘yan bindiga, yanzu wadannan ‘yan ta’adda kamar sun samu mafaka a hukumance.

Masana tsarin yaki sun tabbatar babu yakin da za a iya nasara idan makiyinka yana da mazauni a kofar gidanka.

Wadannan ‘yan ta’addar suna dauke da makamansu suna watayawa yadda suke so a yankin.

Sun zama kamar wasu sojojin haya, abokan ta’addancinsu suna gayyatarsu aiki a wasu jihohin su yi su dauki kasonsu su koma.

Wadda ta fi wahala daga wannan mummunan yanayi ita ce Jihar Katsina.

Abin tsoro shi ne nan gaba a fara daukar hayar wadannan ‘yan ta’addar daga daji don aiwatar da kisa ko kashe-kashe don siyasa.

Saboda yanzu suna kara zamanatar da ta’asar tasu a matsayin neman kudi da rayuwa a kan wannan.

Wani lamarin kuma shi ne majiyoyinmu sun tabbatar wa da jaridunmu cewa, gamayyar jami’an tsaro sun yi wa duk wani sansanin ‘yan ta’adda da ke kusa da babban titin Kaduna zuwa Abuja raga-raga.

‘Yan bindigar yanzu sun tarwatse zuwa can cikin daji. Wannan ya sanya suka dauki lokaci ba su yi hari ba, domin sai sun yi doguwar tafiya.

An takura su a dajin da yawan harin. Wadannan miyagun yanzu wasu sun koma bangaren Birnin Gwari, wasu Zamfara wajen ‘yan’uwansu da suke da fahimta da gwamnatin Zamfara da wasu dazuzzukan Katsina.

Wadannan gudaddun masu dauke da makamai duk lokacin da kwayarsu ta motsa, Jihar Katsina ce mafi kusa su murza guminsu.

Katsina na da iyaka da kasar Nijar, jami’an tsaron Nijar ba su yi wa ‘yan bindigar nan da dadi.

Don haka kullum mafakarsu su shiga Zamfara wajen ‘yan’uwansu masu fahimta da gwamnati in sun huta su shigo Katsina su yi ta’addaci.

Majiyarmu a hukumomin tsaro sun tabbatar wa da jaridun mu cewa, har yanzu ‘yan bindigar nan na da wani shiri na kai wa babban birnin Katsina wani hari da zai girgiza Jihar da Kasar baki daya.

Ana kitsa shirin ne daga dajin Zamfara. Wani kasurgumin dan ta’adda da ke da fahimta da gwamnatin Zamfara shi ne ake zargin yake jagorantar shirin.

Kodayake hukumomin tsaro suna aiki ba dare ba rana wajen hana aukuwar hakan. Suna tattara bayanai da kuma katse masu hanzari.

Mene ne mafita? Ta farko, ita ce addu’o’i kala-kala wadda Allah zai ji tausayinmu.

Na biyu, kafa jami’an tsaron kare kai na garuruwa, unguwanni da shiyya. Kowa ya shigo ciki. Wani ya ba da karfin sa, wani kudi, wani addu’a. Kowa ya ba da irin tasa gudunmuwar da zai iya.

Na uku, mu yi fata da addu’a da goyon bayan wani tsarin tsaro da gwamnatin Jiha take son bullo da shi ya yi nasara.

Shirin yanzu haka an ware masa kudi da tsari, kuma har Majalisar Jiha ta amince da shi. Wata runduna ce za a kafa da duk hukumomin tsaro da kuma na kungiyoyinsa kai.

Na hudu, kar ku dogara ga jami’an tsaro su kawo maku dauki. Ku fada wa jami’an tsaro kuna cikin hari, amma ku kare kanku.

Katsina City News
@ www.katsinacitynews.com
Jaridar Taskar Labarai
@ www.jaridartaskarlabarai.com
The Links News
@ www.thelinksnews.com

Share

Related

Source: Katsina City News
Via: Zaharadeen Mziag
Previous Post

DANLAMI KURFI YA SAMU MUKAMI A GWAMNATIN TARAYYA

Next Post

Shin ta yaya kirarin Kano na “Kano Jalla babbar Hausa” ya gurbace?

Next Post
Shin ta yaya kirarin Kano na “Kano Jalla babbar Hausa” ya gurbace?

Shin ta yaya kirarin Kano na “Kano Jalla babbar Hausa” ya gurbace?

Recent Posts

  • Gwamna Masari ya Kaddamar da Kwamitin Miƙa Mulki ga sabuwar Gwamnati
  • Masari: Tinubu Na Bukatar Addu’a
  • Bashin Da Ake Bin Najeriya Ya Karu Zuwa N46.25tr —DMO
  • FEC Approves N59.78bn For Ogoni Cleanup Projects
  • Reports Of Oyo School Invasion By Herdsmen Fake News – Police

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In