• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Zuwan Buhari Katsina: Matasa sun fusata akan takura su da akayi

Katsina City News by Katsina City News
January 26, 2023
in Sashen Hausa
0
Zuwan Buhari Katsina: Matasa sun fusata akan takura su da akayi
0
SHARES
175
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Muhammad A. Aliyu @Katsina City News

Ranar Alhamis 26 ga watan Janairu shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bude wasu muhimman Ayyukan raya ƙasa a garin Katsina, wanda Mai girma Gwamnan Katsina Rt.Hon Aminu Bello Masari yayi da suka haɗa da Titin Kurɗe guda biyu na Kofar Kwaya da Kofar Kaura, Ofishin Karbar Haraji na jiha, Gidan Ruwa, da Gyaran Babbar Asibitin jihar Katsina sai Kamfanin Shinkafa na Alhaji Dahiru Barau Mangal.da gini a makarantar koyon fasahar yanayi ta gwamnatin tarayya.da habaka bunkasa watsa ruwan Sha a birnin katsina da babban asibitin katsina da aka daga darajar shi da Kuma Yi masa kwaskwarima

Bayan da Shugaba Muhammadu Buhari ya isa Unguwar Kofar Kaura wanda anan ne ya fara buɗe Titin, sai ya wuce Babbar tashar samar da ruwa dake da nisan akalla mita 400 ko fiye, daga bakin sabon titin a can ma ya bude.

An samu Tankiya a tsakanin Matasan inda bayan shugaba Buhari ya bar wajen suka fito daga sako da Lungunan da aka tsare aka hana wucewa suna cewa “Bamu so, bama yi” wanda ya haifar da Jefe-jefe da Ƙona taya, inda har aka gaggaɓe kankaren Silaf mai ɗauke da Hatimin suna da ranar da Shugaban ya bude wannan Titi.

Katsina City News, sun tattara bayanai ta bakin mazauna Unguwar da masu shagunan kayan sana’a a wajen, wanda suka bayyana mana cewa, “An takurasu an hanasu kasuwanci, sana an hanasu ko leƙawa suga yanda taron ke gudana”

Da muke zantawa da wani a bakin Banki wajen ATM don cirar kudi da ya ki bayyana sunansa yace “Mutane na cikin kunci ka ganni nan tun Asuba nazo na cire kuɗi amma kaga ni-ne na 116, mun shiga halin rayuwa da matsatsi, sana jami’an tsaro sun zo sun takura mana saboda zuwan Shugaban Ƙasa, nema ma ake mu bar bakin Bankin sai shugaban yazo ya tafi.” Yace yana tsammanin hadda wannan ne ya haddasa mutane suka hassala.

Wani kuma cewa yayi lallai ba’aimasu adalci ba saboda matsalar Canza kudi, shiyasa ma kowa ke Allah wadai da shugaban.

Katsina City News ta fahimci mafiya yawa daga masu Allah wadai da ziyarar suna Danganta abin da matsin Canza kuɗi da suke fuskanta.

Shugaban ya samu rakiyar Gwamna Aminu Masari da manyan jami’an Gwamnatinsa.

Share

Related

Source: Katsina City News
Via: Katsina City News
Previous Post

HOODLUMS IN ƊANMARKE ATTACK APC CAMPAIGN TRAIN

Next Post

Tsokaci akan Muhawarar da BBC Hausa ta shirya tsakanin masu takarar kujerar gwamnan jihar katsina a Karkashin jamiyyu mabanbanta,

Next Post
Muhawarar BBC Hausa a Katsina: “Abokan Takarata Basu Shirya Amsar Gwamnati ba” -Engr. Nura Khalil

Tsokaci akan Muhawarar da BBC Hausa ta shirya tsakanin masu takarar kujerar gwamnan jihar katsina a Karkashin jamiyyu mabanbanta,

Recent Posts

  • Hajj 2023: Azman begins airlift of pilgrims Today
  • Hajj Airlift: NAHCON Airlift 14,000 pilgrims in 33 flights operations, set up back up plans
  • Hajj 2023: Plateau pilgrims “stranded’ over “failure to remit funds” for Hajj officials
  • Abin da aka tattauna a taron Tinubu da gwamnonin Jam’iyyar APC
  • Makkah service providers pledges ‘memorable’ Hajj 2023 for Nigerian pilgrims

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • June 2023
  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.