• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Friday, March 31, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Za Mu Kawo Nasarar Jam’iyyar PDP A Kowane Mataki A Nijeriya. -Wasu Manyan Kungiyoyi Sun Sha Alwashi.

October 10, 2022
in Sashen Hausa
0
Za Mu Kawo Nasarar Jam’iyyar PDP A Kowane Mataki A Nijeriya. -Wasu Manyan Kungiyoyi Sun Sha Alwashi.
0
SHARES
9
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga Mohammad A. Isa, Katsina.

Wasu manyan kungiyoyin Jam’iyyar PDP a jihar Katsina, sun doki kirji tare da shan alwashin kawo rumfunan zabuka tare da samun nasararorin jam’iyyar adawa ta PDP a jiha da ma kasa baki daya.

Gamayyar kungiyoyin Ladon Alkhairi da kungiyar nan mai rajin tallata dan takarar jam’iyyar PDP a Kasa ‘PDP National Youth Vanguard Katsina State Chapter’ a turance ne suka bayyana haka a yayin wani taron sada zumunci da hadin gwiwa a ranar Lahadi.

A yayin da yake jawabi a taron, shugaban kungiyar ta ‘PDP National Youth Vanguard’ na jihar Katsina, Alhaji Umar Misbahu Mai Zare, ya ce sun yi wannan hada-ka ne na hada hannu da karfe domin cin nasarar zabukan 2023 da ake fuskanta, inda a cewarsa za su kawo wa jam’iyyarsu ta PDP rumfuna a kowane mataki a jiha da kasa baki daya.

“Muna da Capacity da za mu hada hannu da karfe domin kawo nasarar jam’iyyar PDP a kowane mataki a Nijeriya.” Ya doki kurji.

Ya ci gaba da cewa, “Babu wanda zai kalli mulkin da PDP ta yi wanda Matawallen Katsina Alhaji Umaru Musa ‘Yar’adua ya jagoranta shekara 8 ya ce akwai ragganci a cikinsa. Babu wanda zai kalli mulkin shekaru 8 da Barista Ibrahim Shehu Shema ya yi ya ce akwai raggwanci a cikinsa. Kuma kowa ya kallin wannan mulki da ake yi yanzu (na APC), ya san mulki ne wanda yake cike da raggwanci.” Ya gwalashe.

Shi ko a nasa jawabin, shugaban kungiyar Ladon Alkhairi, Honorabul Musa Yusuf Gafai ya bayyana jin dadinsa a kan yadda wannan kungiya wadda take uwa ga kaf din kungiyoyin jam’iyyar PDP, amma ta karbi kungiyarsa ta kuma ba ta muhimmancin gaske har suka dauke ta a matsayin lamba daya a wajensu, inda ya bayyana hakan a matsayin jam’iyyar PDP ce mai nasara a zabukan 2023.

Musa Gafai, ya kuma karfafa ‘ya’yan kungiyoyin biyu da duk wani dan jam’iyyar PDP da cewa; “kar mu bari abin nan (mulkin APC) ya zarce!”

A yayin taron hadin gwiwar kungiyoyin biyu, kungiyar Ladon Alkhairi, ta bada takardar ‘appointment’ na wasu mukamai, muhimman takardu da ‘Tags’ na girmamawa ga wasu ‘ya’yan kungiyar ta National Youth Vanguard.

Share

Related

Source: Katsina City News
Via: Zaharaddeen
Previous Post

Sauyin Sheka: An Kona Tsintsiya A Mashi.

Next Post

An Bayyana Kungiyar Lado Alkhairi A Matsayin Kungiyar Da Babu Kamarta A Jam’iyyar PDP.

Next Post
An Bayyana Kungiyar Lado Alkhairi A Matsayin Kungiyar Da Babu Kamarta A Jam’iyyar PDP.

An Bayyana Kungiyar Lado Alkhairi A Matsayin Kungiyar Da Babu Kamarta A Jam'iyyar PDP.

Recent Posts

  • On birthday, clerics pray for Tinubu, Nigeria in Abuja
  • Gwamna Masari ya Kaddamar da Kwamitin Miƙa Mulki ga sabuwar Gwamnati
  • Masari: Tinubu Na Bukatar Addu’a
  • Bashin Da Ake Bin Najeriya Ya Karu Zuwa N46.25tr —DMO
  • FEC Approves N59.78bn For Ogoni Cleanup Projects

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In