• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

YANZU-YANZU: Ana zanga-zanga kan
shirin kawo tsohon shugaban jami’an tsaro na Ganduje a matsayin Kwamishinan Ƴansanda na Kano

Katsina City News by Katsina City News
March 7, 2023
in Sashen Hausa
0
YANZU-YANZU: Ana zanga-zanga kanshirin kawo tsohon shugaban jami’an tsaro na Ganduje a matsayin Kwamishinan Ƴansanda na Kano
0
SHARES
16
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Magoya bayan jam’iyyar adawa ta NNPP a jihar Kano sun fara zanga-zanga kan shirin kawo Balarabe Sule, tsohon babban jami’in tsaro na gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, zuwa Jihar Kano a matsayin kwamishinan ‘yan sanda.

Tsohon shugaban hukumar TETFUND, kuma tsohon ɗan takarar Sanata na Kano-ta-Arewa, Baffa Bichi ne ke jagorantar zanga-zangar.

DAILY NIGERIAN ta samu rahoton cewa masu zanga-zangar sun yi tsinke a shelkwatar ƴansanda ta shiyya da ke kan titin BUK a kwaryar birnin Kano.

Tun a jiya Litinin ne wasu sahihan majiyoyi su ka shaida wa DAILY NIGERIAN cewa in dai ba wani canji aka samu ba, Sufeto-Janar na ƴansanda zai kawo Balarabe Sule ya maye gurbin Mohammed Yakubu, wanda aka tura jihar makonni biyu kacal da suka wuce.

Wasu daga cikin ‘yan sanda sun tabbatar wa DAILY NIGERIAN cewa, Sufeto Janar na ‘yan sandan Najeriya Usman Alkali, ya bayar da umarnin tura jami’in ‘yan sandan jihar, biyo bayan matsin lamba da jam’iyya mai mulki ta ke yi masa.

Majiyar mai tushe ta shaida wa wannan jarida cewa za a tura MSule zuwa jihar Kano tare da ACP Abubakar Shika da ACP Adamu Babayo.

Sule, wanda a kwanan nan aka kara masa mukami zuwa na kwamishinan ƴansanda, aka kuma kai shi jihar Cross River, ya kasance mataimakin kwamishinan ‘yan sanda mai kula da ayyuka a Kano tsawon shekaru da dama.

A cewar masu lura da al’amuran cikin gida, jami’an ukun, wadanda dukkansu suka yi aiki tare, an yi musu tambarin da cewa su na da bamgaranci na siyasa, inda da ake amfani da su wajen murkushe ‘yan adawa.

Majiyoyin sun shaidawa DAILY NIGERIAN cewa wannan wani shiri ne ke yi wajen sarautar da martabar aikin su domin hada kai da ƴan siyasa wajen murkushw jam’iyyun adawa.

A tuna cewa a sake zaben gwamna na 2019, an hada kai da ƴansanda wajen bai wa ‘yan baranda masu biyayya ga jam’iyya mai mulki damar hargitsa zaben, tare da kai wa masu kada kuri’a, masu sa ido kan zabe da ‘yan jarida hari.

Share

Related

Source: Daily Nigerian
Via: Katsina City News
Previous Post

ANALYSIS: Governorship Poll: Yar’adua’s men go to war over Katsina top seat

Next Post

Tinubu: Surmounting the odds and healing the wounds

Next Post
Tinubu: Surmounting the odds and healing the wounds

Tinubu: Surmounting the odds and healing the wounds

Recent Posts

  • Ƙungiyar ‘Yan jarida ta Najeriya za ta fara yajin aiki kan cire tallafin mai
  • Nigeria Loses 965 Soldiers, Policemen To Boko Haram, IPOB In 2 Years
  • Gbajabiamila ya gode wa Tinubu bisa naɗa shi shugaban ma’aikata
  • Tinubu ya jajanta wa Indiya kan hatsarin jiragen ƙasa
  • Hajj 2023: Azman begins airlift of pilgrims Today

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • June 2023
  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.