• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Friday, March 31, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home General Stories

‘Yan Bindiga Sun Sace Tsohon Darakta Da Mutane 50 A Neja

July 23, 2022
in General Stories, Sashen Hausa
0
0
SHARES
1
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

‘Yan bindiga sun sace Tsohon Daraktan Kula da Ma’aikata na Jihar Neja, Alhaji Usman Abdullahi Malami da Likitan dabbobi, Musa Mohammed, da ke Ma’aikatar kula da dabbobi, tare da wasu mutane 50 da’ yan bindiga suka sace a jihar Neja.

Rahotanni sun tabbatar da cewa, ‘yan bindigar sun sace mutanen ne a yankunan Kananan Hukumomin Kontagora da Munya.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa masu garkuwa da mutanen sun sace Malami ne ranar Juma’a a lokacin da yake dawowa gida a hanyar Kontagora-Mariga, tare da wasu ma’aikatan da suke aiki tare da shi.

Shi ma Dakta Muhammad an sace shi ne a kan hanyar dawowa Kontagora daga kauyukan yankin inda ya je don yi wa dabbobi allura.

Daga bisani ‘yan bindigar da suka sace mutanen sun kira iyalansu, inda suka nemi a biya su Naira miliyan 15 a matsayin kudin fansa.

A ‘yan kwanakin nan dai ‘yan bindiga sun matsa kaimi wajen kai hare-hare kan jama’a a kan hanyoyin Kontagora-Mariga da Kontagora-Rijau, inda suke kashewa da sace jama’a.

A wani labarin kuma, ‘yan bindigar sun sace mutane 50 a garuruwan Kuchi a Karamar Hukumar Muna a Jihar Neja.

A wata sanarwa da jami’in gudanarwa na kungiyar matasan Shiroro

(Concerned Shiroro Youths), Sani Kokki, ya raba wa manema labarai, ya ce an sace mutanen ne da karfe 2 na daren Juma’a.

“Mun samu rahotannin da ke tabbatar da cewa ‘yan ta’adda masu yawan gaske sun kai hari wasu kauyuka a yankin Kunchi a Karamar Hukumar Munya a tsakar dare, inda suka sace mutane masu yawan gaske”, in ji shi.

Kokki ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun ci karensu babu babbaka, inda suka rika bi gida-gida suna sace mutane a daidai lokacin da ake ruwan sama. Ba su kashe kowa ba, amma sun sace mutane akalla 50.

Kokki ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun ci karensu babu babbaka, inda suka rika bi gida-gida suna sace mutane a daidai lokacin da ake ruwan sama. Ba su kashe kowa ba, amma sun sace mutane akalla 50.

Kwamishinan Tsaro, Jin Dadi da Walwalar Jama’a, Emmanuel Umar, ya tabbatar da sace mutanen.

Sai dai kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN), ya jiwo Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Neja, Bala Kuryas, yana cewa jami’an tsaron hadin gwiwa sun yi nasarar ceto mutane tara daga cikin mutanen da aka sace.

Share

Related

Previous Post

A CENTENARIAN BAREWA COLLEGE OF ZARIA

Next Post

I don’t kidnap, I only kill people – Aleru, Zamfara terrorist ‘chief’

Next Post

I don’t kidnap, I only kill people – Aleru, Zamfara terrorist ‘chief’

Recent Posts

  • On birthday, clerics pray for Tinubu, Nigeria in Abuja
  • Gwamna Masari ya Kaddamar da Kwamitin Miƙa Mulki ga sabuwar Gwamnati
  • Masari: Tinubu Na Bukatar Addu’a
  • Bashin Da Ake Bin Najeriya Ya Karu Zuwa N46.25tr —DMO
  • FEC Approves N59.78bn For Ogoni Cleanup Projects

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In