• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Monday, January 30, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Tsohon Sakataren Gwamnatin jihar Katsina Dakta Mustapha Inuwa ya Kaddamar da Kungiyar Matasan PDP a Mazabar Wakilin Arewa “A” Cikin Birnin Katsina.

January 2, 2023
in Sashen Hausa
0
Tsohon Sakataren Gwamnatin jihar Katsina Dakta Mustapha Inuwa ya Kaddamar da Kungiyar Matasan PDP a Mazabar Wakilin Arewa “A” Cikin Birnin Katsina.
0
SHARES
35
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

A ranar Litinin 2 ga watan Janairu Tsohon Sakataren Gwamnatin jihar Katsina kuma jigo a jam’iyyar PDP ya shiga Mazabar Wakilin Arewa A dake Cikin Birnin Katsina domin ƙaddamar da kungiyar Matasan PDP na yankin.

Taron da aka gudanar a Unguwar Madawaki ya samu halartar Wakilan ‘Yan takarar Majalisar Tarayya Hon. Aminu Chindo, da na jiha, tare da jiga-jigai na jam’iyyar PDP a Katsina da Mazabar ta wakilin Arewa A.

Da yake gabatar da Makasudin Kafa wannan Kungiyar, Shugaban Kungiyar Malam Bilya ya bayyana dalilin su na kafa kungiyar da kuma abinda ya kara masu karfin gwiwa na ganin kungiyar ta dore har zuwa zaben 2023.

Yace ” Anyi zaben shekara 2015 Allah bai bawa PDP Nasara ba, hakan yasa wasu daga cikin Abokai suka tuntubeni da cewa yakamata azo a samar da wata kungiya da zata tafi da Murya daya a cikin PDP don ganin hakan bata sake faruwa ba.”

Bilya ya bayyana mutanen da suka tuntubeshi kuma suka bashi jagorancin wanda ta kokarinsu da tuntubar wasu manya a jam’iyyar yasa gashi yanzu kungiyar tayi karfi da rassa a yankin na wakilan Arewa A. Injishi.

Da yake tsokaci a wajen taron tsohon Sakataren Gwamnatin jihar Katsina kuma Daraktan yakin neman Zaɓen Atiku da Lado Danmarke a jihar Katsina, dakta Mustapha Inuwa ya bayyana Kungiyar a matsayin mai ra’ayi da manufa wadda kwadai bai shamata kai ba. Yace “Alokacin da PDP ta faɗi zaɓe makwaɗaita da masu neman muƙami da basu iya adawa ba sukaita gudu don komawa sabuwar Gwamnati a dama dasu, amma ku a lokacin ma kuka yi nazari kuka ga yakamata ku sake Lale ku gyara abinda aka rasa domin daura damara dan neman sake dawo da jam’iyyar a kan mulki.” Yace lallai kam kun ciri tuta a irin wannan kokari.

Dakta Mustapha Inuwa ya gabatar da kungiyar gami da basu shedar karramawa a lokacin da itama kungiyar ta karramashi da lambar yabo.

Taron da ya gayyato masu ruwa da tsaki, a ciki kungiyar ta bayyana cewa zata samar wa Mazabar kuru’u masu tarin yawa bisa tsarin da sukayi.

Tun daga farko Jigo a jam’iyyar PDP Malam Ayuba Gambarawa ya bayyana jin dadi da gamsuwarsa ga kungiyar, gami da yabon kokarin da Dakta Mustapha Inuwa yake a cikin jam’iyyar PDP don ganin samun Nasarar zaben 2023, a karshe yayi fatan Alkhairi ga daukacin mahalarta taron gami da kira akan jajircewa da samar da ruwan kuru’u a lokacin zaɓe.

Share

Related

Source: Katsina City News
Via: Katsina City News
Previous Post

Malaman addinin Musulunci na Nijeriya sun yi ta’aziyyar mutuwar Fafaroma Benedict

Next Post

Kamar Kullum;📸 Ƙungiyar Asiwaju Gwagware gida-gida Initiative a garin Ɓatagarawa

Next Post
Kamar Kullum;📸 Ƙungiyar Asiwaju Gwagware gida-gida Initiative a garin Ɓatagarawa

Kamar Kullum;📸 Ƙungiyar Asiwaju Gwagware gida-gida Initiative a garin Ɓatagarawa

Recent Posts

  • APC ta gano kafafen yada labaran da PDP ke ɗaukar nauyi su yaɗa karya a kan Tinubu
  • Emefiele: We’ve collected N1.9trn old naira notes so far — N900bn more to go
  • Hanyoyi Shida Domin Kiyaye Basir Cikin Sauƙi.
  • Bankin CBN Ya Samar Da Naira Miliyan 120 Domin Yin Canjin Kudi A Katsina.
  • INEC ta kara tsawaita wa’adin karbar katin zabe

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In