• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

TSIGE MATAIMAKIN SHUGABAN KARAMAR HUKUMA, KUSKUREN SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR KURFI A BISA DOKA.

Katsina City News by Katsina City News
May 4, 2023
in Sashen Hausa
0
TSIGE MATAIMAKIN SHUGABAN KARAMAR HUKUMA, KUSKUREN SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR KURFI A BISA DOKA.
0
SHARES
15
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Nazarin jaridun Katsina City News, lokacin da aka zabi Alhaji Mannir Shehu Ruma, Shugaban Karamar Hukumar Kurfi dattawan garin sun dauka cewa a matsayinsa na Malamin makaranta zai yi kokarin ganin cewa doka da tsari sun tabbata a Karamar Hukumar, abubuwa na ta faruwa a Karamar Hukumar wadanda ke ba su mamaki, amma tsige mataimakin Shugaban Karamar Hukumar ba tare da bin dokar da take rubuce ba.

Ya kara tabbatar wa da mutanen garin cewa alwalarsa akwai lam’a. Mece ce ka’idar tsige mataimakin Shugaban Karamar Hukuma? Ga abin da doka ta ce;

  1. Ana iya tsige Shugaban Karamar Hukuma ko mataimakinsa a bisa tsarin wannan sashen.
  2. Rubutaccen korafi, wanda wasu mambobin na Majalisar Zartarwa suka sanya wa hannu.
  3. Zargin da ake yi wa wanda ake tuhuma za a sanar wa duk ’yan Majalisar a rubuce za a sake aika wa wanda ake zargi a rubuce don ya kare kansa cikin kwanaki bakwai.
  4. Bayan mako biyu da aika wa wanda ake tuhuma da takardarsa, Majalisar Zartarwa za su zauna su yanke shawarar ci gaba da tuhumar, ko kuma a kyale maganar.
  5. Idan har aka yanke shawarar a ci gaba da tuhumar, sai an samu amincewar kashi biyu cikin uku na ’yan Majalisar Zartarwar.
  6. In Majalisar Zartarwar ta amince da ci gaban binciken za ta aika wa Babban Mai Shari’a na Jihar domin ya kafa kwamitin mutane bakwai da za su binciki zargin.
  7. Wanda ake zargin zai iya kare kansa ko ya dauki Lauya da zai tsaya masa.
  8. Kwamitin yana da tsawon watanni uku ya kammala aikinsa da bayar da rahotansa.
  9. Idan kwamitin ya kasa tabbatar da zargin, daga nan aikin kwamitin ya tsaya.
  10. Idan wancan kwamitin da Babban Mai Shari’a ya kafa ya samu wanda ake zargi da laifin, Majalisar Zartarwar tana da tsawon makon biyu ta dau matsayar cire shi ko kyale shi. Idan har suka cire shi ya ciru har abada.
  11. In har aka bi wadannan ka’idojin babu wata kotu da za ta iya sauraren karar wanda aka cire.

Wadannan sune ka’idojin da ke cikin kundin dokokin kananan hukumomi na shekarar 2000 na Jihar Katsina, wanda Shugaban Karamar Hukumar Kurfi ya yi fatali da su wajen tsige mataimakinsa.

Katsina City News. www.katsinacitynews.com. Jaridar Taskar Labarai. www.jaridartaskarlabarai.com. The Links News. www.thelinksnews.com.

Share

Related

Source: Katsina City News
Via: Katsina City News
Previous Post

BINCIKEN MUSAMMAN:MULKIN KAMA KARYA A KARAMAR HUKUMAR KURFI

Next Post

’Yan Luwadi 5 Sun Shiga Hannu A Nasarawa

Next Post
’Yan Luwadi 5 Sun Shiga Hannu A Nasarawa

’Yan Luwadi 5 Sun Shiga Hannu A Nasarawa

Recent Posts

  • Hajj 2023: Azman begins airlift of pilgrims Today
  • Hajj Airlift: NAHCON Airlift 14,000 pilgrims in 33 flights operations, set up back up plans
  • Hajj 2023: Plateau pilgrims “stranded’ over “failure to remit funds” for Hajj officials
  • Abin da aka tattauna a taron Tinubu da gwamnonin Jam’iyyar APC
  • Makkah service providers pledges ‘memorable’ Hajj 2023 for Nigerian pilgrims

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • June 2023
  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.