• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Taron Haɗin Gwiwa APC da NNPP an bawa Hamata Iska a Katsina.

Katsina City News by Katsina City News
March 9, 2023
in Sashen Hausa
0
Jam’iyyar NNPP ta goyi bayan Takarar Dikko Radda a Katsina.
0
SHARES
118
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Zaharaddeen Ishaq Abubakar, Fatima Sa’ad @Katsina City News

Da Yammacin ranar Alhamis ne, Jiga-jigai na Jam’iyyar NNPP mai kayan Marmari, suka shirya wata ganawa da bayyana goyon bayansu ga Dan takarar Gwamnan Katsina na Jam’iyyar APC Dakta Dikko Umar Radda a Ɗakin Taro na MUNAJ dake daura da gidajen Fatima Shema.

Taron wanda ya tattara ‘Ya’yan jam’iyyar NNPP daga Ƙananan Hukumomi 34 na jihar Katsina, gami da shugaban Jam’iyyar NNPP Hon. Sani Liti ‘Yan Kwani, Dan takarar Mataimakin Gwamnan jiha a NNPP Engr. Muttaƙa Rabe Darma, Dan takarar Sanata NNPP daga Shiyyar Daura, Sanata Abdu ‘Yandoma, da sauran magoya bayansu. Sai tawagar Dakta Dikko Umar Radda da suka halarci taron, a ciki akwai shi Dan takarar na Gwamna Dakta Dikko Umar Radda da Mataimakinsa Hon. Faruq Joɓe, Shugaban Yakin Neman Zaben na Dakta Dikko Radda, ARC. Ahmed Dangiwa, Umar tsauri, da Kwamishina Ruwa na jihar Katsina.

Shugaban yakin neman zaben na Dakta Dikko Umar Radda yayi cikakken bayani game da murna ta wannan hadin gwiwa tsakanin NNPP da APC, ya bayyana cewa sun ji dadi sunyi Farinci na ganin ‘Yayan Jam’iyyar NNPP sun fahimci Manufofin Dakta Dikko Umar Radda kuma har suka yadda su mara masa baya don cimma Nasara, yace sunyi Maraba da farinciki da komawarsu APC.

Saidai a tsakar taron, magoya bayan Jam’iyya NNPP sun bayyana cewa an yaudaresu saboda ba a sanar dasu abinda za’ayi ba, kuma anyimasu balilliba. Inda suka tada hatsaniya, wanda daƙar aka shawo kansu.

Da Dan takarar Mataimakin Gwamna a karkashin Jam’iyyar NNPP Engr. Muttaƙa Rabe ya amshi abin magana ya bayyanawa magoya bayansu cewa, su basun zo nan don su koma NNPP ba, a’a sam sunzo ne don su bayyana cewa zasu marawa Dikko Radda baya, a APC don ya zama Gwamna ba don komai ba sai dan ya cancanta kuma mutum ne, mai sanin Yakamata da Ilimi. Yace suna nan jam’iyyarsu ta NNPP kuma zasu ci gaba da tarairayarta har takai lokacin da zasu moreta.

Dakta Dikko Umar Radda ya gabatar da Jawabin godiya da nuna jin dadi bisa wannan yarda da Amincewa da magoya bayan NNPP sukai masa, kuma ya tabbatar da Insha Allah ba zai basu kunya ba.

Saidai bayan taron ya tashi, magoya bayan na NNPP sunyi ka-ce-na-ce harda bige-bige, kafin wani dan lokaci sai ga Dan takarar Gwamna a NNPP Engr. Nura Khalil ya bayyana a wajen inda ya ƙaryata zancen kuma yace shi ba da yawunsa ba. Wannan magana tasa bata yiwa magoya bayan Muttaƙa Rabe Dadi ba, inda anan aka fara bawa Hamata Iska, hatta ‘yan takarar suma suka sanya hannu.

Abin ya tsagaita duk da babu wasu jami’an tsaro a wajen, mun samu zantawa da Dan takarar Gwamna Engr. Nura Khalil, ya sheda wa Katsina City News cewa, ba da yawunsa ba bai sanda maganar ba, ankirashi ne, akace Engr. muttaƙa da Shugaban Jam’iyyar NNPP zasu cefanar da Takararsa. Shine yazo wajen don ya ƙaryata zancen. Nura Khalil ya bayyana cewa har yanzu yana kan takara kuma zasu dauki mataki akan masu yunkurin Lalatamsu jam’iyya a cikin satinan Sana ya bayyana jin dadinsa na dage zaben da akayi na Gwamna, yace hakan zai basu damar gane Munafukai jam’iyyar NNPP a Katsina.

Share

Related

Source: Katsina City News
Via: Katsina City News
Previous Post

Jam’iyyar NNPP ta goyi bayan Takarar Dikko Radda a Katsina.

Next Post

Ba a son rai na na kashe Ummita kuma ina roƙon kar a kashe ni, in ji ɗan China

Next Post
Ba a son rai na na kashe Ummita kuma ina roƙon kar a kashe ni, in ji ɗan China

Ba a son rai na na kashe Ummita kuma ina roƙon kar a kashe ni, in ji ɗan China

Recent Posts

  • Ƙungiyar ‘Yan jarida ta Najeriya za ta fara yajin aiki kan cire tallafin mai
  • Nigeria Loses 965 Soldiers, Policemen To Boko Haram, IPOB In 2 Years
  • Gbajabiamila ya gode wa Tinubu bisa naɗa shi shugaban ma’aikata
  • Tinubu ya jajanta wa Indiya kan hatsarin jiragen ƙasa
  • Hajj 2023: Azman begins airlift of pilgrims Today

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • June 2023
  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.