• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Friday, March 31, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Sufuri: Matafiya Daga Wasu Garuruwa Sun Shiga Halin Ha’ula’e Sanadiyyar Ƙin Karɓar Tsofaffin Takardun Kuɗi Ko Transfer

March 17, 2023
in Sashen Hausa
0
Sufuri: Matafiya Daga Wasu Garuruwa Sun Shiga Halin Ha’ula’e Sanadiyyar Ƙin Karɓar Tsofaffin Takardun Kuɗi Ko Transfer
0
SHARES
22
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga Muhammad Aminu Kabir

Adai dai lokacin da Mutane da dama suke ruguguwar barin garuruwan da suke domin zuwa jihohin su suyi zaɓe adai dai lokacin kuma suke cin karo da aƙuba a tashoshin mota sanadiyyar rashin tsabar takardun kuɗi.

Rashin Sababbin takardun kuɗi ya tsunduma Mutane da dama cikin rashin tabbas yayin da kuma masu tsofaffin takardun kuɗi ma aka ƙi karɓar nasu duk kuwa da yake cewa fadar Shugaban ƙasa da babban bankin ƙasa sun Amince cewa a ci gaba da karɓar tsofaffin takardun kuɗin amma dai har yanzu Mutane suna ɗari ɗarin karɓar su.

Matafiya da dama sukaje tashoshin mota mallakin Gwamnatin Jihar Katsina a garuruwan da suke da zummar tahowa gida sun haɗu da wannan ƙalubale, Inda ga motoci amma an bayyana cewa wai Operation Manager daga KATSINA yace ba’a amsar transfer ba’a kuma amsar tsofaffin takardun kuɗi.

Abin mamaki kuma gwamnatin jihar Katsina na ɗaya daga cikin Gwamnatocin da suka kai gwamnatin tarayya ƙara a kotu domin a cigaba da amsar tsaffin kuɗi amma ga motochin hukumar Gwamnatin Jihar basa karɓar tsofaffin takardun kuɗin idan kabasu, Duk dako kotu ta bada Umarnin amsa, gwamnatin tarayya ta bada umarni amsa, Central bank ya bada umarni karɓa, Amma abun mamaki KTSTA idan ka basu basa karɓa komi nene dalilin hakan Allah masani.

Kodai a jiya Motocin Hukumar daga jihar Kaduna zuwa Katsina sun ki amsar tsofaffin takardun kuɗin kazalika transfer, dalilin da yasa Matafiya da dama halin ƙunci, munyi ƙoƙarin jin ta bakin Babban Manajan hukumar ko akwai dalilin da yasa basa karɓar tsofaffin takardun kuɗin sai dai ya aiko da saƙon cewa yana Meeting har kawo wannan lokacin kuma bai maido kira ba.

Sai dai a wuri ɗaya kuma Sakataren hukumar Sufurin ta jihar Katsina Alh. Ibrahim Ahmed Keegan ya bayyana cewa a babban Offishin Hukumar dake nan Katsina suna amfani da P.O.S domin sauƙaƙa ma Matafiya amma dai a wajen jihar ne basu da pos ɗin batun rashin karɓar transfer kuma yace gaskiya ana samun damuwa da ita ne mafi yawan lokaci ta kan ɗauki lokaci bata sauka ba a wani lokacin ma Ƴan 419 suna amfani da yanayin suce sun tura alhalin basu tura ba, sai dai yace baida Masaniya akan mi yasa ba’a amsar tsofaffin takardun kuɗin amma dai zai bincika.

Haƙiƙa an wahalar da jama’a a motochin gwamnati kuma Mutanen katsina wanda da dama suna tafiya ne KATSINA domin suyi zaɓe, Amma idan kazo da tsaffin kuɗi sai suƙi karɓa.

Kiran da muke ga wannan Hukumar dama Gwamnatin Jihar Katsina shine su dubi Lamarin nan domin samar ma Mutane mahita adai dai wannan yanayin da aka rutso na matsin tattalin arziki sanadiyyar wannan rashin takardun kuɗin a hannun jama’a.

Share

Related

Source: Culled from Aminu Kabir Page
Via: Katsina City News
Previous Post

INEC ta yi alkawarin gudanar da zabe na gaskiya da adalci

Next Post

Ashe Amaryar Da Ake Cewa Ta Yi Kankanta Bazawara Ce?

Next Post
Ashe Amaryar Da Ake Cewa Ta Yi Kankanta Bazawara Ce?

Ashe Amaryar Da Ake Cewa Ta Yi Kankanta Bazawara Ce?

Recent Posts

  • On birthday, clerics pray for Tinubu, Nigeria in Abuja
  • Gwamna Masari ya Kaddamar da Kwamitin Miƙa Mulki ga sabuwar Gwamnati
  • Masari: Tinubu Na Bukatar Addu’a
  • Bashin Da Ake Bin Najeriya Ya Karu Zuwa N46.25tr —DMO
  • FEC Approves N59.78bn For Ogoni Cleanup Projects

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In