• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Friday, March 31, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

RANAR VALENTINE TA SHEKARAR 1991 A JAMI’AR ABU ZARIYA

February 15, 2023
in Sashen Hausa
0
RANAR VALENTINE TA SHEKARAR 1991 A JAMI’AR ABU ZARIYA
0
SHARES
5
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga Danjuma Katsina

A rana mai kamar ta yau ce, na jagoranci wasu dalibai Musulmi muka tarwatsa gungun wasu dalibai da ke bukin ranar Valentine a Sculpture Garden da ke ABU Zariya.

Wannan lamarin ya faru ne a daren 14 ga watan Fabrairu, 1991.

Mu shida muka kitsa farmakin. Ni, Danjuma; wanda na tsara na kuma shugabanta, sai Ibrahim Potiskum, Abdulmumini Giwa; yanzu shi ne Editan Jiha na jaridun VANGUARD a Kano, Dakta Samir Yusuf; yanzu yana koyarwa a ABU Zaria, Muhammad Balkore; yanzu yana Abuja, Alhaji Mamu; yana Abuja, bayan ya gama karatun Likita a kasar Iran, sai wadanda suka rufa mana baya.

Mun tsara komai ne a babban masallacin Juma’a na ABU, amma daga dakin su Malam Ibrahim Potiskum da ke Magume 4, Room 5.

Bayan kai farmakin kungiyar dalibai Musulmi ta Jami’ar sun yi Allah wadai da aikinmu, suka nemi Hukumar makaranta ta dau mataki a kanmu.

A lokacin ina cikin zababbu shugabannin kungiyar dalibai Musulmi na Jami’ar a matsayin Editan Mujallar Kungiyar da ake kira THE WISDOM.

A ranar 16 ga Fabrairu, 1991 kwana biyu bayan farmakin ranar Valentine na kira taro a babban masallacin Juma’ar Jami’ar, inda na shelanta rusa shugabancin kungiyar dalibai Musulmi na Jami’ar da kafa wani kwamiti da zai rika sa ido a kan harkokin dalibai Musulmi na jami’ar kafin a gudanar da sabon zabe. Sunan kwamitin, Shura Committee.

Kwamitin Shura shi ne ya jagoranci bukin kona Mujallun LOLLY da FUNTIMES a Jami’ar ta ABU, saboda wani rubutu da zane na cin zarafin Manzon Allah (SAW).

Rikicin ya yadu kusan duk manyan makarantun kasar nan, wanda ya haifar da wata shela a Katsina, inda Gwamnan soja na lokacin ya ce zai sanya a kama Malam Yakubu Yahaya ya kai shi filin Polo ya harbe shi.

Rayuwa ke nan. Allah ya kara mana kwanaki masu albarka da taimakon Musulunci da al’umma baki daya.

Danjuma Katsina 14/2/2023

Share

Related

Source: Katsina City News
Via: Katsina City News
Previous Post

Despite Buhari’s Endorsement, Tinubu Won’t Win Katsina – Ex-NHIS Boss

Next Post

Kotun Koli Ta Dage Sauraron Kara Kan Canjin Kudi

Next Post
Kotun Koli Ta Dage Sauraron Kara Kan Canjin Kudi

Kotun Koli Ta Dage Sauraron Kara Kan Canjin Kudi

Recent Posts

  • On birthday, clerics pray for Tinubu, Nigeria in Abuja
  • Gwamna Masari ya Kaddamar da Kwamitin Miƙa Mulki ga sabuwar Gwamnati
  • Masari: Tinubu Na Bukatar Addu’a
  • Bashin Da Ake Bin Najeriya Ya Karu Zuwa N46.25tr —DMO
  • FEC Approves N59.78bn For Ogoni Cleanup Projects

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In