• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

NNPP ta yi kira da a hukunta Ciyaman ɗin APC da aka kama da katukan zaɓe 300 a Kano

Katsina City News by Katsina City News
October 15, 2022
in Sashen Hausa
0
NNPP ta yi kira da a hukunta Ciyaman ɗin APC da aka kama da katukan zaɓe 300 a Kano
0
SHARES
6
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Jam’iyyar adawa ta NNPP da kungiyoyin farar hula, ƙarƙashin inuwar ‘Alliance for Good Governance’ sun bukaci da a gaggauta gurfanar da wani shugaba a jam’iyyar APC, Aliyu Shana da aka kama da katin zaɓe na dindindin guda 300 a Kano.

Shana, wanda shi ne shugaban jam’iyyar APC na unguwar Yautan Arewa, Ƙaramar Hukumar Gabasawa a jihar Kano, ya shiga hannun ƴan sanda a jiya Juma’a, tare da mika shi zuwa shelkwatar rundunar domin bincikar sa.

DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa mallakar katin zabe ba bisa ka’ida kuma na ɗauke da sunan wasu ya saɓa wa sashe na 21 da 22 karamin sashe na 1 (a), (b) da (c) na dokar zaɓe ta 2022 da aka yi wa kwaskwarima.

A wata sanarwa da shugaban NNPP na jihar, Umar Doguwa ya fitar, ya ce jam’iyyar ta umurci lauyoyin ta da su shigar da kara a kan wanda ake zargin da kuma waɗanda su ka sa shi ya aikata.

“Na umarci mai ba mu shawara kan harkokin shari’a da ya rubuta wa alkalan zabe (INEC) don bibiyar matakin da ya dace a kan lamarin,” in ji Doguwa.

Ya ce batun ɓoye katin zabe na PVC ya zama babban abin damuwa a Kano gabanin zaben 2023.

“Wannan kamen ya tabbatar da gaskiyarmu mu, za kuma mu tsaya tsayin-daka mu ga matakai na gaba da hukumar zabe mai zaman kanta da ƴan sandan Nijeriya za su dauka,” inji shi.

Jam’iyyar NNPP ta ce za ta ci gaba da bin shari’ar har zuwa tiƙewa domin kare martabar dimokuradiyya.

Shugaban jam’iyyar ya yaba da kokarin da rundunar ƴan sandan jihar Kano ke yi na tabbatar da gudanar da bincike mai inganci kan lamarin.

Share

Related

Source: Kano Media Post
Via: Zaharadeen
Previous Post

Gwamna Masari ya janye Dokar hana hawa mashina da karfe goman dare

Next Post

Yajin Aikin ASUU: Muna Neman Afuwar Dalibai Da Iyaye – Gwamnatin Tarayya

Next Post
Yajin Aikin ASUU: Muna Neman Afuwar Dalibai Da Iyaye – Gwamnatin Tarayya

Yajin Aikin ASUU: Muna Neman Afuwar Dalibai Da Iyaye – Gwamnatin Tarayya

Recent Posts

  • Dr. Dikko sworn in as Governor, takes over from Masari in Katsina State.
  • Tinubu Ya Nada Dele Alake A Matsayin Mai Magana Da Yawunsa
  • In inaugural address, Tinubu preaches unity, commitment to nation-building
  • Jawabin Farko a Matsayin Shugaban ƙasa: Tinubu ya cire Tallafin Mai gaba ɗaya
  • Malam Dikko Umar Radda ya zama sabon gwamnan jihar Katsina

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.