• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Karbo Bashin $800m Zalunci Ne —Sani Brothers Ga Buhari

Katsina City News by Katsina City News
May 19, 2023
in Sashen Hausa
0
Karbo Bashin $800m Zalunci Ne —Sani Brothers Ga Buhari
0
SHARES
15
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Sani Brohers ya bukaci gwamnati ta sake tunani, domin babu abin da karbo bashin zai yi illa cutar da jama’ar kasar nan

Fitaccen dan kasuwa a Najeriya, Alhaji Sani Yunusa Sarina (Sani Brothers) ya ce zalunci ne shirin Gwamnatin Tarayya na karbo bashin Dala miliyan 800 daga Bankin Duniya domin rage radadin janye tallafin man fetur da za ta yi.

A kwanakin baya ne Shugaba Buhari ya nemi sahalewar majalisar dokoki ta kasa don karbo bashin domin raba wa talakawa da nufin rage musu radadin cire tallafin mai da gwamnatinsa ta so yi.

Amma a yayin hirarsa da ’yan jarida a Kano, Alhaji Sani Brothers, wanda tsohon Shugaban Kungiyar Masu sufuri ta Kasan ne ya bukaci gwamnati da sake tunani, domin a babu amfanin da karbo bashin zai yi, sai da ma ya cutar da jama’ar Najeriya.

A cewarsa, “Ban taba ganin inda aka karbo bashi aka yi kyauta ba. Ta yaya za a karbi bashi a ba wasu tsiraru wanda ba su fi kaso 10 cikin 100 ba, sannan a bar nauyin biyan bashin a kan alummar kasa gaba daya, wadanda ba su ci ba, ba su sha ba?”

A cewar Alhaji Sani Brothers, za a iya cire tallafin mai ba tare da ciyo bashi da kuma rabawa ga wasu tsiraru ba.

“Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo ya cire tallafin mai kuma bai karbo bashin ko kwabo ba har daga baya aka dawo da tallafin.

“To me ya sa ita wannan gwamnatin za ta fito da wannan magana, ko ita nata shirin daban ne?”

Ya ci gaba da cewa karbo bashin ba zai amfanar da alumma ba, illa cutuwa gare su.
“Ya kamata shugabanni su daina kawo abubuwan da za su cutar da talakawansu. Wannan bashi cutarwa ce ga talakawan domin kasarsu ce za ta biya.

“Kuma ba su ne za su amfana da kudin ba, wasu ne wadanda ba talakawan ba za su amfana da bashin.”

Tsohon bashi ba ne —Bankin Duniya

Bankin Duniya, ta bakin daraktansa a Najeriya, Shubham Chaudhuri, ya bayyana cewa bashin ba sabo ba ne, kuma tun watan Dismanban shekarar 2021 mahukuntan bankin suka amince da bakatar Najeriya ta karbar rancen.

Shubham Chaudhuri ya kara da cewa, karba ko kin karbar kudin hurumin ne na gwamnati mai jiran gado, kuma majalisa na da ikon amincewa ko watsi da bukatar sa hannu.

A cewarsa, samun izinin majalisar da Buhari ke yi ne zai saukaka wa sabuwar gwamnati amfani da kudaden idan tana bukata, domin bayar da tallafin janye tallafin man fetur.

Chaudhuri, ya ce “idan sabuwar gwamnatin za ta janye tallafin mai, za ta iya karbar kudaden babu bata lokaci, maimakon sai ta sake komawa neman sahalewar majalisa.

“Wannan gwamnatin saukin karbar kudaden kawai take nema wa wadda za ta gaje ta, idan har tana da ra’ayin janye tallafin man.

“Idan ba haka ba, sai an samu karin akalla wata shida ana kai-komo a kai kafin Kwamitin Daraktocin Bankin Duniya su amince.

“Haka kuma, idan kuma sabuwar gwamnati ba ta bukatar rancen, za ta iya soke bukatar, sannan ko da majalisa ta amince a karbo, ba dole ne gwamnatin ta karbo kudaden ba.”

Share

Related

Source: Aminiya
Via: Katsina City News
Previous Post

Read the Full Report of General Abdulsalam Abubakar Committee on Kano State Emirate Crisis

Next Post

Karo na Ukku: An Yaye Jami’an Sa Kai don tabbatar da Tsaro a Katsina

Next Post
Karo na Ukku: An Yaye Jami’an Sa Kai don tabbatar da Tsaro a Katsina

Karo na Ukku: An Yaye Jami'an Sa Kai don tabbatar da Tsaro a Katsina

Recent Posts

  • Hajj 2023: Azman begins airlift of pilgrims Today
  • Hajj Airlift: NAHCON Airlift 14,000 pilgrims in 33 flights operations, set up back up plans
  • Hajj 2023: Plateau pilgrims “stranded’ over “failure to remit funds” for Hajj officials
  • Abin da aka tattauna a taron Tinubu da gwamnonin Jam’iyyar APC
  • Makkah service providers pledges ‘memorable’ Hajj 2023 for Nigerian pilgrims

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • June 2023
  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.