• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Friday, March 31, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Jihohin da ba za a yi zaɓen gwamna ba a ranar Asabar

March 17, 2023
in Sashen Hausa
0
Jihohin da ba za a yi zaɓen gwamna ba a ranar Asabar
0
SHARES
21
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

©️BBC Hausa

Yayin da ake shirin kaɗa ƙuri’a a zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisun jiha a Najeriya a ranar Asabar mai zuwa, akwai wasu jihohi na daban guda shida da ba za a yi zaɓen gwamna a cikinsu ba.

Jihohin su ne:

Anambra

Bayelsa

Edo

Ekiti

Kogi

Ondo

Osun.

Wannan ya biyo bayan hukuncin kotu na rushe wasu zaɓuka da aka yi a baya tare da tabbatar da wasu da aka zaɓa waɗanda da farko ba su aka bayyana ba a matsayin masu nasara.
Sai dai a duka jihohin za a gudanar da zaɓen ‘yan majalisun jiha kamar yadda aka tsara tun da fari.

Wannan rashin daidaiton zaɓe tsakanin jihohin shida da sauran jihohin ƙasar ya zamar wa hukumar zaɓe ta INEC wani abu na koma baya, ganin kowacce jiha sai dai a yi mata nata shirin daban.

Hakan dai ya samo asali ne tun a 2003 lokacin da aka gudanar da zaɓen jihar Anambra a watan Afrilu.

Aka bayyana Dr. Chris Ngige na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaɓe, aka kuma rantsar da shi a matsayin gwamna ranar 29 ga watan Mayu na 2023, tare da duk wanda aka zaɓa.

A wannan lokaci Peter Obi ne ke takarar gwamnan jihar a jam’iyyar APGA, ya nuna bai gamsu da wannan sakamako ba, abin da ya kai shi ga shigar da ƙara gaban kotu kenan.

Bayan shekara uku ya samu nasara kan shari’ar da ya shigar gaban kotun sauraren ƙararrakin zaɓe, a ƙarshe dai a watan Maris na 2006 a ka rantsar da shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen jihar.

Ko da aka zo gudanar da zaɓe a 2007, Obi bai shiga zaɓen ba, hakan ya sanya aka bayyana Andy Uba a matsayin wanda ya lashe zaɓen ƙarakashin jam’iyyar PDP.

Daga baya kotu ta ƙara yanke hukuncin cewa Obi ne gwamna domin wa’adin mulkinsa bai ƙare ba, ta kuma yi bayani kan cewa “ wa’adin gwamna na farawa ne kawai daga ranar da aka rantsar da shi,” in ji kotu.

Tun daga wannan lokaci ne aka samu sabani wajen gudanar da zaɓe a jihar ta Anambra.

Irin wannan lamari ne ya faru a jihar Edo a ranar 14 ga watan Afrilun 2007, lokacin da kotun saurarren kararrkin zaɓe ta ayyana Adams Oshiomhole a matsayin wanda ya lashe zaɓen jihar kuma ‘yan taccen gwamna.

A 2010 ma, haka aka yi lokacin da kotu ta ayyana Kayode Fayemi a matsayin gwamnan Ekiti, ba a sake zaɓe a jihar ba sai 2014, maimakon 2011.

A watan Agustan 2008, kota a jihar Ondo ta ayyana Dr. Olusegun Mimiko na jam’iyyar LP a matsayin gwamnan da ya lashe zaɓen jihar.

Kotun ta kwace mulki ne daga hannun Olusegun Agagu na jam’iyyar PDP wanda aka rantsar tare da sauran waɗanda suka ci mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2007.

Irin waɗannan tarin matsaloli da shari’u ne suka taru suka haifar da jinkiri a wajen daidaita zaɓe tsakanin waɗannan jihoji da sauran da za a gudanar da zaɓensu a ranar Asabar 18 ga watan Maris.

Share

Related

Source: BBC Hausa
Via: Katsina City News
Previous Post

Abin Da Zan Yi Idan Tinubu Ya Ba Ni Mukami A Gwamnatinsa -Peter Obi

Next Post

Ahead Of Tomorrow’s Polls: Security Operatives On Red Alert In States

Next Post
Zaɓen gwamna: An tura ƴansanda dubu 18,748 zuwa Kano

Ahead Of Tomorrow’s Polls: Security Operatives On Red Alert In States

Recent Posts

  • On birthday, clerics pray for Tinubu, Nigeria in Abuja
  • Gwamna Masari ya Kaddamar da Kwamitin Miƙa Mulki ga sabuwar Gwamnati
  • Masari: Tinubu Na Bukatar Addu’a
  • Bashin Da Ake Bin Najeriya Ya Karu Zuwa N46.25tr —DMO
  • FEC Approves N59.78bn For Ogoni Cleanup Projects

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In