• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Saturday, January 28, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Iyayen ɗaliban makarantar Yauri da aka sace sun fara yin karo-karo don kuɓutar da ƴaƴansu

January 11, 2023
in Sashen Hausa
0
Iyayen ɗaliban makarantar Yauri da aka sace sun fara yin karo-karo don kuɓutar da ƴaƴansu
0
SHARES
9
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Iyayen sauran ɗalibai 11 da a ka yi garkuwa da su a Kwalejin Gwamnatin Tarayya da ke garin Yauri a Jihar Kebbi, sun fara shiri na tara kudin fansa Naira miliyan 100 domin a sako ƴaƴansu.

Jaridar DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa a ranar 17 ga watan Yuni, 2021, aka sace dalibai sama da 80 a lokacin da wasu ‘yan bindiga, karkashin jagorancin wani ƙasurgumin ɗan fashin jeji, Dogo Gide suka kai hari makarantar.

Daga baya an sako yawancin daliban ga gwamnatin jihar bayan an biya kudin fansa.

Sai dai bayan watanni 19 ‘yan ta’addan na ci gaba da tsare 11 daga cikin daliban, inda suke neman kudin fansa Naira miliyan 100.

Da suke magana da jaridar Daily Trust a ranar Lahadi, iyayen daliban da aka sace da suka hadu a harabar makarantar sun koka kan yadda suka yanke shawarar daukar al’amura a hannunsu bayan gwamnati ta gaza musu.

Shugaban kungiyar iyayen, Salim Kaoje, ya bayyana cewa sun tattauna da Gide tare da taimakon mahaifiyar sa, wadda ya ce tana kara matsa masa lamba kan ya sako ƴan matan.

“Mun tattauna da Dogo Gide ne a ranar 15 ga watan Disamba 2022, da farko ya ki amincewa da duk wani yunkurin tattaunawa da mu, amma bayan da mahaifiyarsa ta shiga tsakani, ya amince ya sako yaran mu idan muka biya kudin fansa naira miliyan 100, in ba haka ba, ba za mu sake ganin ƴaƴan mu ba.

“Ya bayyana karara cewa idan har ba mu hada kuɗin da ya nema ba, ba za mu sake gani ko jin ɗuriyar ‘ya’yanmu ba, kuma wannan ne ya sa muka taru a matsayin iyaye domin yin wannan roko,” inji shi.

Kaoje ya ce kowanne daga cikin iyayen ya kuduri aniyar sayar da duk wani abu da ya mallaka da suka hada da kadarorin kasa da sauran kayayyaki masu daraja, domin samun damar tara kuɗin don a sako ƴaƴan na su.

Share

Related

Source: Daily Nigeria
Via: Katsina City News
Previous Post

POLICE PRESS RELEASE: BURSTING/ARREST OF A THREE (3) MAN KIDNAP FOR RANSOM SYNDICATE AND RESCUE OF A KIDNAP VICTIM

Next Post

INEC ta fara tantance waɗanda suka cike aikin zabe a jihar Katsina yau Laraba

Next Post
INEC ta fara tantance waɗanda suka cike aikin zabe a jihar Katsina yau Laraba

INEC ta fara tantance waɗanda suka cike aikin zabe a jihar Katsina yau Laraba

Recent Posts

  • Buhari inaugurates 12 projects in Katsina
  • ZA AYI TAGWAYEN HANYOYI DAGA KOFAR SORO ZUWA KOFAR GUGA
  • PRESS STATEMENT: Old Naira Notes:Kano Govt,Islamic Clerics Calls On Federal Govt To Extend Naira Redesign Deadline
  • Sanarwa! Sanarwa!! Sanarwa!!! Hukumar Sufuri ta KTSTA zataci gaba da amsar tsaffin kudi
  • Dala Inland Dry Port: Kanawa Ga Na Ku
    By Adamu S. Ladan

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In