• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Friday, March 31, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Cire Tallafin Man Fetur Kafin 29 Ga Watan Mayu

March 16, 2023
in Sashen Hausa
0
Gwamnatin Tarayya Za Ta Cire Tallafin Man Fetur Kafin 29 Ga Watan Mayu
0
SHARES
50
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Ministar Kudi, Kasafi da Tsare-Tsare ta Kasa, Misis Zainab Ahmed, ta ce gwamnatin tarayya za ta cire tallafin man fetur da ake ta cece-kuce a kan shi kafin karshen wa’adin shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar 29 ga Mayu, 2023.

Zainab ta danganta jinkirin cire tallafin kamar yadda dokar masana’antar man fetur (PIA) ta tanadar a shekarar 2021, ga babban zaben 2023 da kuma kidayar al’ummar kasa da ke tafe.

Ministar ta bayyana haka ne a yayin wata ziyarar ban girma da ta kai hedikwatar VON da ke Abuja.

Sai dai a jiya gwamnatin tarayya ta bayyana cewa har yanzu ba a cimma matsaya ba kan yadda za a dakile illar shirin cire tallafin man fetur ga ‘yan kasar nan ba.

Haka zalika, ta bayyana a jiya cewa hukumar kula da albarkatun man fetur ta Ghana NPA ta cire tallafin man fetur a kasar.

A jiya ne gwamnatin Nijeriya ta dage kidayar yawan jama’a da gidaje na shekarar 2023, wadda tun farko ta shirya a karshen wannan watan zuwa watan Mayu, sannan ta amince da ajandar Nijeriya ta 2050, da ke da nufin mayar da kasar nan mai karfin tattalin arziki.

Zainab ta bukaci gwamnati mai jiran gado da ta kara kudin haraji (VAT) daga kashi 7.5 yanzu zuwa kashi 10.

Ta ce cire tallafin abu ne mai wahala a siyasance da tattalin arziki da gwamnati ta dauka.

Sai dai ministar ta ce kusan kowa a yanzu ya amince cewa tallafin ba ya yi wa mutanen da ya kamata hidima kuma tsadarsa na kara gibi a gwamnatance.

Ta kara da cewa kudin tallafin litar man fetur ya kai tsakanin N350 zuwa N400, inda Nijeriya ke kashe kusan Naira biliyan 250 a kowane wata wajen bayar da tallafin.

Share

Related

Source: Leadership Hausa
Via: Katsina City News
Previous Post

Dan Majalisar Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Fita Yakin Neman Zabe A Bauchi

Next Post

Abin Da Zan Yi Idan Tinubu Ya Ba Ni Mukami A Gwamnatinsa -Peter Obi

Next Post
Abin Da Zan Yi Idan Tinubu Ya Ba Ni Mukami A Gwamnatinsa -Peter Obi

Abin Da Zan Yi Idan Tinubu Ya Ba Ni Mukami A Gwamnatinsa -Peter Obi

Recent Posts

  • On birthday, clerics pray for Tinubu, Nigeria in Abuja
  • Gwamna Masari ya Kaddamar da Kwamitin Miƙa Mulki ga sabuwar Gwamnati
  • Masari: Tinubu Na Bukatar Addu’a
  • Bashin Da Ake Bin Najeriya Ya Karu Zuwa N46.25tr —DMO
  • FEC Approves N59.78bn For Ogoni Cleanup Projects

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In