• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Gwamnati Za Ta Cefanar Da Asibitin Fadar Shugaban Kasa

Katsina City News by Katsina City News
May 1, 2023
in Sashen Hausa
0
Gwamnati Za Ta Cefanar Da Asibitin Fadar Shugaban Kasa
0
SHARES
27
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

An ware wasu bagarori na Fadar Shugaban Kasa da gwamnati za ta fara yin hadaka da ’yan kasuwa wajen gudanar da su

Gwamnatin Tarayya ta fara shirin cefanar da Asibitin Fadar Shugaban Kasa da wasu sassa da ke karkashin fadar gwamnatin ga ’yan kasuwa.

Babban Sakataren Fadar Shugaban Kasa, Tijjani Umar, ya ce Ma’aikatar Kudi da Kasa tare da Fadar Shugaban Kasar sun ware wasu ayyuka da tsare-tsare uku a Fadar Shugaban Kasa da gwamnati za ta fara yin hadaka da ’yan kasuwa wajen gudanar da su.

Ya bayyana cewa Asibitin Fadar Shguaban Kasa da ke Abuja da Legas daya ne daga bangarorin da ake shirin shigo da ’yan kasuwa su zuba jari.

Sauran su ne Sashen Kula da Gandun Daji da kuma Dandalin Wasan Yara na Fadar Shugaban kasa.
Tijjani Umar ya sanar da haka ne a jawabinsa ga taron wata uku na farkon shekarar 2023 kan hadakar gwamnati da kamfanoni da ya gudana a Fadar Shugaban Kasa.

A baya yanayin da Asibitin Fadar Shugaban Kasa ke ciki ya tayar da kura, musamman bayan da matar shugaban kasa, Aisha Buhari ta yi korafi game da rashin magunguna da kayan aiki a asibitin.

’Yan Najeriya na yawan yin ce-ce-ku-ce game da yadda Shugaba Buhari ke zuwa duba lafiyarsa a kasashen waje.

A watannin baya Shugaba Buhari ya sanya aikin gina sabbin bangarori na bayar da kulawa ta asibitin na musamman a kasafin 2023.

A watannin baya dai Gwamnatin Tarayya ta yi kokarin yin dokar hana jami’an gwamnati zuwa duba lafiyarsu a kasashen waje, da nufin inganta yanayin bangaren lafiyar Najeriya.

Bangaren lafiyan Najeriya na fama da karancin likitoci, inda kwararrun likitoci ke tururuwar barin kasar domin yin aiki a kasashen waje.

Kungiyar likitoci ta Najeriya (NMA) ta bayyana cewa kasa da likitoci 15,000 ne suka rage a kasar mai yawan al’umma sama da miliyan 200.

A kan haka ne majalisar dokoki ta kasa take kokarin yin dokar da zai wajabta wa wadanda suka kammala karatu a fannin likita yin aiki aiki na shekara biyar a kasar kafin a ba su lasisi.

Share

Related

Source: Aminiya
Via: Katsina City News
Previous Post

2023 UTME: JAMB announces date for rescheduled exams

Next Post

Workers’ Day: Organised Labour advocates review of retirement age

Next Post
Workers’ Day: Organised Labour advocates review of retirement age

Workers’ Day: Organised Labour advocates review of retirement age

Recent Posts

  • Ƙungiyar ‘Yan jarida ta Najeriya za ta fara yajin aiki kan cire tallafin mai
  • Nigeria Loses 965 Soldiers, Policemen To Boko Haram, IPOB In 2 Years
  • Gbajabiamila ya gode wa Tinubu bisa naɗa shi shugaban ma’aikata
  • Tinubu ya jajanta wa Indiya kan hatsarin jiragen ƙasa
  • Hajj 2023: Azman begins airlift of pilgrims Today

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • June 2023
  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.