• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Gwamna Masari ya kaddamar da fara gina Titi a Karamar hukumar Danja

admin-admin by admin-admin
September 1, 2022
in Sashen Hausa
0
Gwamna Masari ya kaddamar da fara gina Titi a Karamar hukumar Danja
0
SHARES
32
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Hanya na daya daga cikin abinda ke habbaka arziki agari, Inji Masari.

Maigirma Gwamnan Jihar Katsina ya fadi hakan ne lokacin da ya kaddamar da fara aikin gina hanya mai nisan kilo mita (25) a garin Kokami dake cikin karamar hukumar Danja, Jihar Katsina .

Gwamna Masari yace wannan aikin hanya zai fara daga Garin Danja, Bazanga har zuwa Nahuce da Kokami, haka kuma ya kara da cewa aikin zai lakume zunzurutun kudi kimanin naira Biliyan biyu da miliyan dari hudu.

Gwamna Masari a lokacin kaddamar da fara gina hanyar

Gwamna Aminu Bello Masari ya cigaba da cewa wannan aiki nada nufin inganta rayuwar al’umma musamman mutanen Karamar Hukumar Danja , domin yin hanyar zai kara haffaka arzikin Karamar hukumar tare da inganta harkar noma, Gwamnan yayi kira ga yan karamar hukumar Danja musamman wadanda zasu amfana da aikin hanyar, da su kula da aikin da kuma bada goyon baya ga masu aikin domin samun nasarar aikin.

Haka kuma, Gwamnan ya yi kira ga Kamfanin da zai gudanar da aikin, da ya yi aiki mai nagarta , kuma ya tabbatar da kammala aikin cikin wata (18) kamar yadda aka kulla yarjejeniya da yankwangilar.

Daga karshe Gwamna yayi godiya ta musamman ga Babban jagoran shirin na kasa injiniya Aminu Muhammed Bodinga abisa zabar Jihar Katsina acikin wannan shiri .

Shima a nashi jawabin, Kwamishinan ma’aikatar kula da muhalli ta Jihar Katsina Hon. Hamza Sule Faskari ya bayyana cewa” za’a gudanar da aikin Karkashin shirin samar da hanyoyi a karkara da bunkasa amfanin gona mai suna yima ( RAAMP).

Ya kuma cigaba da bayyana kokarin Gwamnatin Aminu Bello Masari na inganta muhalli a fadin Jihar, na gina magudanan ruwa a fadin Jihar, daga karshe yayi godiya ta musamman abisa irin goyon bayan da Maigirma Gwamna yake ba ma’aikatar wanda wannan ne yasa take samun nasarar gudanar da ayyukanta cikin nasara.

Tun farko da yake gabatar da jawabin maraba, Shugaban shirin na Jihar Katsina Injiniya Falalu Husaini ya bayyana cewa “wannan aiki hanya shi ne na farko a fadin kasar nan karkashin wannan shiri”.
Ya cigaba da cewa “za’a gina hanyar da kwalbatoci, da magudanan ruwa”. ya cigaba da cewa “idan an kammala aikin ana sa ran za ta samar da hanyar shiga yankunan cikin sauki ba tare da wani cikas ba a kowane lokaci da yarda Allah.

Dayake jawabin, Shugaban shirin na kasa baki daya Injiniya Aminu Muhammed Bodinga yace “wannan aiki shi ne na farko, amma akwai wasu da dama na nan zuwa. Shima yayi kira ga Al’umma da su bada hadin kai da goyon baya.
Daga karshe yayi godiya ta musamman ga Gwamnatin Maigirma Shugaban Gasa Muhammadu Buhari tare kuma da jinjinama Maigirma Gwamna Aminu Bello Masari abisa kokarin da yake na ingata rayuwar al’umma. Shima a nashi jawabin Dan Majalisa mai wakiltar karamar hukumar Danja Hon. Shamsuddeen Abubakar Dabai ya godema ma Maigirma Gwamna abisa wannan aiki da aka kawo masu.

A nashi jawabin Wakilin Kamfanin na “Mother Cat” da zasu gudanar da aikin, ya yi godiya akan yadda aka ba Kamfanin damar gudanar da wannan aiki tare da yin alkawarin kiyaye yarjejeniyar da aka kulla. Dan haka zasu tabbatar dayin aiki mai kyau kuma mai inganci, zasu Kuma tabbatar da sun kammala aikin cikin watanni (18) kamar yadda akayi yarjejeniya dasu.

Daga karshe Shugaban karamar hukumar Danja, Hon. Rabo Tambaya ya yi jawabin godiya tare da fatan alheri ga Gwamnatin Alh Aminu Bello Masari abisa kulawar da Gwamnatin take masu.

Daga ofishin Darakta Janar, Sabbin Kafofin Sadarwa na zamani na Maigirma Gwamnan Jihar Katsina.
1/9/2022.

Share

Related

Source: Katsina
Via: Katsina City News
Previous Post

Bahaushe Ya Zama Manjo Janar A Rundunar Sojojin Kasar Sudan

Next Post

Anyiwa Sojoji Kwantan Bauna a tsakanin Jibiya zuwa Gurbi

Next Post
Gwamnatin Katsina zata gina hanyar Danja Nahuce, zuwa Bazanga. 

Anyiwa Sojoji Kwantan Bauna a tsakanin Jibiya zuwa Gurbi

Recent Posts

  • Dr. Dikko sworn in as Governor, takes over from Masari in Katsina State.
  • Tinubu Ya Nada Dele Alake A Matsayin Mai Magana Da Yawunsa
  • In inaugural address, Tinubu preaches unity, commitment to nation-building
  • Jawabin Farko a Matsayin Shugaban Æ™asa: Tinubu ya cire Tallafin Mai gaba É—aya
  • Malam Dikko Umar Radda ya zama sabon gwamnan jihar Katsina

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.