• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Friday, March 31, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

DSS Ce Abokiyar Hamayarmu A Kano Ba APC Ba —NNPP

March 16, 2023
in Sashen Hausa
0
DSS Ce Abokiyar Hamayarmu A Kano Ba APC Ba —NNPP
0
SHARES
13
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Jam’iyyar ta zargi cewar DSS na hada kai da APC don murde zabe a jihar.

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta bayyana cewa Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS) ce babbar abokiyar hamayarta ba APC ba.

NNPP ta yi zargin hukumar na aiki tare da jam’iyyar APC mai mulkin jihar domin tauye muradin jama’a a zaben gwamna da za a gudanar a ranar Asabar.

Da yake jawabi a madadin NNPP, Baffa Bichi, dan takarar kujerar Sanata a jam’iyyar, ya ce magoya bayan NNPP sun shirya tattaki na lumana a fadin jihar don nuna rashin amincewarsu kan ci gaban Daraktan DSS da zama ofishinsa bayan lokacin ritayarsa ya yi, wata 15 da suka shude.

Jam’iyyar ta kuma yi zargin cewa Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ne ya bukaci a aike da daraktan  DSS din a 2017, sannan shi ya roki ya ci gaba da zama duk da karewar wa’adin aikinsa.

Ta kuma yi zargin cewa an aike da wasu jami’an DSS na musamman daga Abuja don taimaka APC wajen murde zabe.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne DSS ta sanar da kama wasu magoya bayan NNPP guda biyu kan zargin yunkurin tada tarzoma gabanin zaben ranar Asabar.

Kakakin DSS, Peter Afunanya, ya sanar a ranar Alhamis cewa an kama Sharu Abubakar Tabula da Isma’il Iliyasu Mangu ne kan zargin su da tunzura jama’a a kafafen sada zumunta.

Takun sakan DSS da NNPP

A baya dai an samu rashin jituwa tsakanin NNPP da DSS tun bayan da matar Darakta-Janar na DSS, Yusuf Bichi, ta yi sa-in-sa da dan takarar gwamnan Kano a NNPP, Abba Kabir Yusuf.

Rikicin ya fara ne bayan da ayarin motocin Abba sun tare wa ayarin matar Yusuf Bichi hanyar shiga dakin manyan baki a filin jirgin saman Malam Aminu Kano.

Hakan ta kai ga cece-ku-ce tsakanin matar shugaban DSS din da wasu magoya bayan NNPP kafin daga bisani jami’an tsaro suka shiga tsakani.

Gabanin zaben shugaban kasa, DSS ta kai samame ofishin NNPP a Kano, abin da jam’iyyar ta zargi jami’an DSS da neman shafa wa magoyanta kashin kaji.

Share

Related

Source: Aminiya
Via: Katsina City News
Previous Post

’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Taron APC

Next Post

Dan Majalisar Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Fita Yakin Neman Zabe A Bauchi

Next Post
Dan Majalisar Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Fita Yakin Neman Zabe A Bauchi

Dan Majalisar Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Fita Yakin Neman Zabe A Bauchi

Recent Posts

  • On birthday, clerics pray for Tinubu, Nigeria in Abuja
  • Gwamna Masari ya Kaddamar da Kwamitin Miƙa Mulki ga sabuwar Gwamnati
  • Masari: Tinubu Na Bukatar Addu’a
  • Bashin Da Ake Bin Najeriya Ya Karu Zuwa N46.25tr —DMO
  • FEC Approves N59.78bn For Ogoni Cleanup Projects

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In