• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Monday, January 30, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Dalilin da ya sa na kashe kishiyar mahaifiyata da ɗiyarta -Matashi

January 9, 2023
in Sashen Hausa
0
Dalilin da ya sa na kashe kishiyar mahaifiyata da ɗiyarta -Matashi
0
SHARES
22
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Rundunar ƴan sanda a jihar Kano, ta kama wani matashi mai suna Gaddafi Sagir, bisa zargin kashe kishiyar mahaifiyarsa, da ƴar ta mai shekara takwas.

A wata sanarwa da kakakin ƴan sandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ta ce lamarin ya faru ne a ranar Asabar a Fadama Rijiyar Zaki da ke Karamar Hukumar Ungogo bayan da mahaifin matashin ya dawo ya sami matarsa, Rabi Sagir, da ƴar ta ta, wacce yar riƙo ce, Munawwara, kwance jina-jina.

Sanarwar ta ƙara da cewa bayan da rundunar ‘yan sandan jihar ta samu labarin abin da ya faru, nan take ta aika jami’anta zuwa wajen, inda bayan an kai matar da kuma yarinyar Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad ne likita ya tabbatar da rasuwarsu.

An dai kama wanda ake zargin ne a wani kango a kokari da yake na tserewa ya bar jihar.

A binciken farko da aka gudanar, wanda ake zargin ya amsa laifinsa na yin kisan inda ya ce ya yi amfani da sukun-direba wajen daɓawa kishiyar babar ta sa a wuya da kuma kai sannan ta shake ‘yarta da ɗankwali har sai da ta daina numfashi.

Da ake tambayar sa dalilin aikata kisan, Gaddafi ya ce ya yi hakan ne sabo da marigayiyar ta takura wa mahaifiyarsa.

“Har ta kai ga mahaifiya ta ta bar gidan ta koma garin mu. Ta kuma hada mahaifi na da mahaifiya ta, ta sanya ya na yi mata wulakanci iri-iri. Ni kuma hakan na ɓata min rai,” in ji matashin.

A cewar sa, rigima ce ta kare tsakanin sa da marigayiya Rabi da safe, lokacin da ya zo ɗaukar abinci, inda ya ƙara da cewa shi ne ya ɗauki sukindireba ya buga mata a wuya.

Ya ƙara da cewa ita ma Munawwara ɗin ya shake ta ne da kyalle zani sabo da ta “buga mun taɓarya a ka. Shi ne ita ma ma shake ta.”

Ya ce shi ba ya shaye-shaye kawai dai sharrin zuciya ne ya sanya ya aikata wannan ta’asar.

Sai dai kuma ya nemi a yi masa afuwa.

Share

Related

Source: Daily Nigerian
Via: Katsina City News
Previous Post

Matar Daraktan SSS ta sa an tsare Abba Gida-gida tare da barazanar kashe hadiminsa a filin jirgin sama a Kano

Next Post

“BA SAI MUNJE DUBAI BA KO WASU KASASHE DON SAWO FURNITURES BA KATSINA MUNA DA IRINSU” -Masari

Next Post
“BA SAI MUNJE DUBAI BA KO WASU KASASHE DON SAWO FURNITURES BA KATSINA MUNA DA IRINSU” -Masari

"BA SAI MUNJE DUBAI BA KO WASU KASASHE DON SAWO FURNITURES BA KATSINA MUNA DA IRINSU" -Masari

Recent Posts

  • APC ta gano kafafen yada labaran da PDP ke ɗaukar nauyi su yaɗa karya a kan Tinubu
  • Emefiele: We’ve collected N1.9trn old naira notes so far — N900bn more to go
  • Hanyoyi Shida Domin Kiyaye Basir Cikin Sauƙi.
  • Bankin CBN Ya Samar Da Naira Miliyan 120 Domin Yin Canjin Kudi A Katsina.
  • INEC ta kara tsawaita wa’adin karbar katin zabe

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In