• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Monday, January 30, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Dalibai za su fara zanga-zanga bisa tsare Aminu Mohammed wanda ya yi suka ga Aisha Buhari

December 2, 2022
in Sashen Hausa
0
Dalibai za su fara zanga-zanga bisa tsare Aminu Mohammed wanda ya yi suka ga Aisha Buhari
0
SHARES
9
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Kungiyar dalibai ta kasa, NANS, ta ce za ta fara wata zanga-zangar ta ba ƙaƙƙauta wa a fadin kasa, domin neman a sako wani dalibin Jami’ar Tarayya da ke Dutse a Jihar Jigawa, Aminu Mohammed, wanda aka kama aka kuma kai shi gidan yari a kan wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter yana sukar matar shugaban ƙasa, Aisha Buhari.

A wata sanarwa da shugaban NANS, Usman Barambu, ya sanyawa hannu a jiya Alhamis, kungiyar ta bayyana cewa za a fara zanga-zangar ne a ranar Litinin mai zuwa har sai Mohammed ya samu ƴancinsa.

DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa tun da farko kungiyar dalibin ta nemi afuwar uwargidan shugaban kasar kan abin kunyar da Mohammed ya wallafa a shafinsa na twitter da ya janyo mata da iyalanta, yayin da ta kuma bukaci a sako dalibin.

Sai dai kungiyar ta bayyana cewa ta gaji da bi ta lallami kan a saki Mohammed, inda ta ƙuduri aniyar yin zanga-zanga.

“Mun yi tuntuba da kuma bi ta lallami wanda bai samar da wani sakamako mai kyau ba wajen neman ƴancin Mohammed, don haka za a fara zanga-zangar kamar haka: Litinin, 5 ga Disamba, 2022 a duk fadin kasar nan.

“Sabo da haka a sani cewa zanga-zangarmu za ta ci gaba har sai an sake shi ba tare da wani sharadi ba,” in ji sanarwar.

Share

Related

Source: Daily Nigerian
Via: Katsina City News
Previous Post

TEACHING IN MOTHER TONGUE

Next Post

ƳAN BINDIGA SUNKAI HARI ƘARARE TA ƘARAMAR HUKUMAR BATSARI

Next Post
ba mutane 39 aka sace a Katsina ba – Ƴan sanda

ƳAN BINDIGA SUNKAI HARI ƘARARE TA ƘARAMAR HUKUMAR BATSARI

Recent Posts

  • APC ta gano kafafen yada labaran da PDP ke ɗaukar nauyi su yaɗa karya a kan Tinubu
  • Emefiele: We’ve collected N1.9trn old naira notes so far — N900bn more to go
  • Hanyoyi Shida Domin Kiyaye Basir Cikin Sauƙi.
  • Bankin CBN Ya Samar Da Naira Miliyan 120 Domin Yin Canjin Kudi A Katsina.
  • INEC ta kara tsawaita wa’adin karbar katin zabe

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In