• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

“Da jami’an tsaron mu na nan Katsina karkashin Masari suke da tuni ankawo karshen Matsalar tsaro.”  -Sabo Musa

admin-admin by admin-admin
September 4, 2022
in Sashen Hausa
0
“Da jami’an tsaron mu na nan Katsina karkashin Masari suke da tuni ankawo karshen Matsalar tsaro.”  -Sabo Musa
0
SHARES
21
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Malam Sabo musa mai taimakawa Gwamnan Katsina na musamman akan maido da al’amura Daidai da muhallansu, yayi wannan jawabin ne a wajen bikin rantsar da ‘Ya’yan kungiyar MOPPAN ta kasa reshen jihar Katsina.

Malam Sabo musa yace “Yanzu ba lokacin yin siyasa da matsalar tsaro bane, wannan matsala ce da take bukatar hada kai da duk wani mutum ko daga wace jam’iyya ya fito domin tunkarar kawo karshen wannan matsala.”

Daga dama Malam Sabo Musa zuwa hagu Engr. Muttaqa Rabe

Ya kara da cewa; a da idan zaka kano ko Abuja shekarun baya sai kayi awa biyar ko goma sha, saboda Checking Point, sakamakon irin yanda Boko Haram suka shiga cikin garin Kano suka tada Bom, suka shiga cikin garin Abuja suka tada Bom a Hedkwatar’Yansandan Najeriya, amma yanzu abin yazama Tarihi injishi.

Yace muyi addu’a dama Allah yace zai jarabemu da abubuwa, iri-iri na daga tsoro, da yunwa, da talauci, da zubda jini. Yace idan wadannan matsaloli suka faru, sai Allah yace kuce Innalillahi wa’inna ilaihiraji’una. Saboda haka maganar hada tsaro da siyasa a bari.  S.A Sabo Musa yace yanzu Allah ya kawo mu wani jarabi na Masu garkuwa da mutane, wanda yake bukatar hadin kai ga dukkanin mu domin magance matsalar.

Sabo Musa yace: game da harkar tsaro a nan jihar Katsina kowa yasan abinda ake, ga Sojoji da ‘Yansanda nan, ku kungiyar MOPPAN, Tunda kungiya ce ta wayar da kai, kungiya ce ta ‘Yan Film to yakamata ku karantar da Al’umma cewa, sojojin nan da ‘yansandan nan ba na Gwamnatin jiha bane, na Gwamnatin tarayya ne, suna amsar Umarni daga sama. Yanzu idan mai girma Gwamnan jihar Katsina zaice ga abinda yake so, to sai sun nemi umarni daga sama, yace da na jihar Katsina ne, da nan take zai bada umarni, kai bama Gwamna ba ko Sakataren Gwamnati zai iya bada Umarni, kuma a aikata abinda yadace.

Sabo musa ya ce duk bukatun da ake so game da maganar tsaro gwamnatin jihar Katsina tana badawa, yace don haka lallai ne gareku ku karantar da mutane wannan matsalar, afidda maganar Siyasa, saboda idan barayin nan sunzo dauka, suna daukar dan PDP, suna daukar dan APC daga ko wace jam’iyya kake sai sun dauke ka. Yace su barayinnan babu ruwansu da siyasa, don mi mu kuma zamu dunga dangana abin da siyasa. Malam Sabo Musa yace, idan wannan matsalar tazo babu wanda take ragawa, andauki mai kudi andau Basarake Andau mai mulki andau, talaka, hatta mai fura da Nono, dauka suke.

A karshe yayi kira da babbar mura ga kungiyar cewa su faɗakar musamman matsalolin da mafiya yawa Infomas ne ke haddasa su, don haka kungiyar ta faɗakar akan wannan matsala, ba zance ba ne na soyayya, ko wani abu, yanzu lokaci ne na neman zaman lafiya, a faɗakar da mutane, inyaso idan an samu zaman lafiya komi za’ayi sai aje ayi. Sabo musa ya bada misalai akan irinsu Kasumu yaro, da marigayi Danjuma Katsina da Fina-finan su da litattafan su, yace sunyi rubutun ne a daidai da zamanunsu da irin matsalolin da suke faruwa a wancen zamanin, yace to ashe kunga haka akeyi, domin magance matsalolin da suka addabi zamanin.

Angudanar da bikin rantsuwa a dakin taro na tsohin gidan Gwamnatin jihar Katsina a ranar Lahadi 4 ga watan Satumba 2022.

Share

Related

Source: Katsina City News
Via: Zaharadeen Mziag
Previous Post

ƳAN BINDIGA SUN KAI HARI DA RANA TSAKA CIKIN GARIN BATSARI….. .. Sun shiga garin suna kabbara

Next Post

Dalilin da yasa nafi son yin wakokin Al’adun Hausa -Ibrahim Dan’iro

Next Post
Dalilin da yasa nafi son yin wakokin Al’adun Hausa -Ibrahim Dan’iro

Dalilin da yasa nafi son yin wakokin Al'adun Hausa -Ibrahim Dan'iro

Recent Posts

  • Dr. Dikko sworn in as Governor, takes over from Masari in Katsina State.
  • Tinubu Ya Nada Dele Alake A Matsayin Mai Magana Da Yawunsa
  • In inaugural address, Tinubu preaches unity, commitment to nation-building
  • Jawabin Farko a Matsayin Shugaban ƙasa: Tinubu ya cire Tallafin Mai gaba ɗaya
  • Malam Dikko Umar Radda ya zama sabon gwamnan jihar Katsina

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.