• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

BINCIKEN MUSAMMAN:MULKIN KAMA KARYA A KARAMAR HUKUMAR KURFI

Katsina City News by Katsina City News
May 4, 2023
in Sashen Hausa
0
BINCIKEN MUSAMMAN:MULKIN KAMA KARYA A KARAMAR HUKUMAR KURFI
0
SHARES
278
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga Wakilanmu @Katsina City News

Wani bincike da jaridar Katsina City News ta gudanar, ta gano a dukkanin shugabannin kananan hukumomin da aka zaba a shekarar 2022, Karamar Hukumar Kurfi na daya daga cikin inda ake mulkin-mulaka’u, tare da take duk wata doka da aka shimfida ta tafiyar da mulki.

Wakilan jaridun Katsina City News, sun ziyarci Karamar Hukumar Kurfi a ranakun Talata 3 da kuma Laraba 4 watan Mayu, domin jin ta bakin mutanen Karamar Hukumar a kan irin mulki da zababben Shugaban Karamar Hukumar yake gudanarwa, Alhaji Mannir Shehu wurma.

Ra’ayoyin da jaridun suka tattaro wadansu har da amincewa a dau hoton bidiyonsu kare bai ci. Al’mmar garin sun bayyana Shugaban Karamar Hukumar yana daukar kansa da tafiyar da mulki kamar wani Sarkin sarakuna mai daraja ta daya da wukar yanka.

Ba abin duk wata doka a tafiyar da aikin Karamar Hukumar, mun samu cikakken bayanin yadda ya dakatar da mataimakinsa ba tare da bin kowacce ka’ida da doka ta gindaya ba.

Takardar da muka gani ita ce, a ranar 17 ga watan Afrilu aka rubuta wa VC Nazifi Rabe aka ce an dakatar da shi. A ranar 3 ga watan Mayu, Shugaban Karamar Hukumar ya rantsar da sabon mataimakinsa, wanda ya nada ba tare da bin duk wata ka’ida ba.

A ranar 4 ga watan Mayu aka aika wa da halastaccen mataimakin Shugaban Karamar Hukumar da takardar tsigewa. Kamar yadda dokar kananan hukumomi ta nuna yadda aka tsige Shugaban Karamar da nada wani, hakan da aka yi ya saba wa ka’idar da aka gindaya guda 11.

A dokar da take rubuce, kuma kundin yake hannun kowanne Shugaban Karamar Hukuma, ana iya daukar wata uku zuwa hudu ba a kammala ka’idar cire mataimakin Shugaban Karamar Hukuma ba, amma a Karamar Hukumar Kurfi cikin kwanaki aka kammala komai.

Jaridun Katsina City News sun ga yadda Shugaban Karamar Hukumar ya kori nadadden Kansila mai kula da sashen ayyuka, Mani Ado Kurfi, shi ma ba tare da bin ka’idar da ta dace ba.

Takarda da aka buga aka aika wa kafofin watsa labarai cewa an kore shi bisa zargin da ba a kira shi ya kare kansa ba.

Mai Unguwa Dayyabu Lankasta da shi da Hakimin Kurfi da Mai Garin Kurfi a wayar hannu suka ga takarda na yawo cewa an kore shi daga aikinsa na Mai Unguwa.

Irin wadannan kore-koren sun zama ruwan dare. Wasu da ke jam’iyyun adawa sun yi zargi ana kai masu harin don cutar da su kai tsaye daga Ciyaman din. Misali kanin Alhaji Shu’aibu Iliya, wanda ake kira da Shagali, wanda ya jigo a jam’iyyar APC daga baya ya canza sheka zuwa jam’iyyar NNPP. Ya yi takakarar dan Majalisar Jiha har aka je zabe zagaye na biyu.

Daga zaben su zuwa yanzu, Karamar Hukumar Kurfi ta samu kudi daga gwamnatin Jiha sun kai Naira miliyan 160, amma duk fadin Karamar Hukumar babu aikin Naira miliyan 15 a tsaye.

Tun da aka zabe su, Shugaban bai taba kiran taron yadda za a sarrafa kudin da ake amsowa daga gwamnatin Jiha ba. Takardun da kuma samu na amsar kudin kananan hukumomi daga gwamantin Jihar Katsina sun tabbatar Kurfi ta amshi kudade masu yawa, amma me aka yi da su?

Aikin hanyar Wurma bincikenmu ya gano aiki ne na kai tsaye. Hayar motocin aka dauko daga Karamar Hukumar Dan Musa ana biyan Direba da kudin mai. Ana zargin ana iya fitar da wasu kudaden Karamar Hukumar da sunan aikin.

Ya ake da kudaden harajin da Karamar Hukumar ke samu? Ina kudin da gireda da rola na Karamar Hukumar Kurfi da aka kai kasar Nijar a Jihar Maradi? Domin su samo kudi? Amsar da jaridun Katsina City News suka kasa samu ke nan. Mun yi kokarin magana da Shugaban Karamar Hukumar abin ya ci tura.

A ranar da aka rantsar da haramtaccen mataimakin Wakilanmu na wajen, amma ba su samu magana da shi ba, sun koma ranar 4 ga watan Mayu sun nemi magana da shi, shi ma abin ya ci tura.

Babban Editan jaridun Katsina City News ya kira shi a waya sau hudu, yana yanke ta. Daga baya ya aiko masa da sakon zai kira shi. Kiran da bai masa ba har zuwa rubuta wannan rahoton. @Katsina City News. www.katsinacitynews.com. Jaridar Taskar Labarai. www.jaridartaskarlabarai.com. The Links News. www.thelinksnews.com.

Share

Related

Source: Katsina City News
Via: Katsina City News
Previous Post

Sudan: We Need More Aircraft To Evacuate Nigerians – FG

Next Post

TSIGE MATAIMAKIN SHUGABAN KARAMAR HUKUMA, KUSKUREN SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR KURFI A BISA DOKA.

Next Post
TSIGE MATAIMAKIN SHUGABAN KARAMAR HUKUMA, KUSKUREN SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR KURFI A BISA DOKA.

TSIGE MATAIMAKIN SHUGABAN KARAMAR HUKUMA, KUSKUREN SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR KURFI A BISA DOKA.

Recent Posts

  • Hajj 2023: Azman begins airlift of pilgrims Today
  • Hajj Airlift: NAHCON Airlift 14,000 pilgrims in 33 flights operations, set up back up plans
  • Hajj 2023: Plateau pilgrims “stranded’ over “failure to remit funds” for Hajj officials
  • Abin da aka tattauna a taron Tinubu da gwamnonin Jam’iyyar APC
  • Makkah service providers pledges ‘memorable’ Hajj 2023 for Nigerian pilgrims

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • June 2023
  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.