• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Monday, January 30, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Babu Ɗan Takarar Da Ke Samun Karɓuwa Kamar Sanata Yakubu Lado -injiniya Bashir Sani Dogo

January 9, 2023
in Sashen Hausa
0
Babu Ɗan Takarar Da Ke Samun Karɓuwa Kamar Sanata Yakubu Lado -injiniya Bashir Sani Dogo
0
SHARES
3
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

An bayyana ɗan takarar gwamnan jihar Katsina ƙarƙashin jam’iyyar PDP Sanata Yakubu Lado Ɗanmarke a matsayin mutum ɗaya da ya fi sauran ‘yan takara samun karɓuwa ga jama’ar jihar Katsina.

Wannan kiran ya fito ne daga bakin matashin ɗan siyasa injiniya Bashir Sani Dogo a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Katsina.

Injiniya Bishir ya cigaba da cewa yadda al’umma ke tururuwar shiga jam’iyyar PDP kaɗai ya isa misali akan batun karɓuwar Sanata Yakubu Lado a wannan Iska mai kaɗawa.

“Taron ƙaddamar da yakin neman zaɓen sa da ya gudana a garin Funtua da kuma ƙaramar hukumar Ɓaure ya zama ishara ga jama’a musamman waɗanda ke wannan tafiya ba tare da an ba su kuɗi ba” inji shi

Ya ce, tunda yake siyasa bai taɓa ganin nasara da idansa ba, sai akan ɗan takarar gwamnan jihar Katsina ƙarƙashin jam’iyyar PDP Yakubu Lado Ɗanmarke.

A cewar sa, Sanata Yakubu Lado ɗan kasuwa ne da yasan yadda ake maida naira goma naira dubu, ya ce zai yi amfani da wannan damar da yake da ita wajan bunƙasa tattalin arzikin da walwalar jama’a a jihar Katsina.

Haka kuma ya yi wa Katsinawa albishir da cewa biyan kudin makaranta (jarabawa) da ya gagara a wannan gwamnatin zai dawo kamar yadda aka san shi, ya ce Lado mutum ne mai kishin ilimin da kiwon lafiya da sauran bangarori more rayuwa.

Injiniya Bishir Sani Dogo ya ƙara da cewa Lado na sane da matsalar tsaro wanda ta hana al’umma da dama yin noma da kiwo, amma yana bada tabbacin cewa insha’Allahu Lado zai kawo gagarumin sauyi cikin ƙaƙanin lokacin idan an zaɓe shi.

“Idan ka kula da Sanata Yakubu Lado Ɗanmarke baya juyawa akan abinda ya fi karfin sa, baya kula da masu yi masa hassada da yankan baya, abinda kawai yasa gaba shi ne, Allah ke bada mulki ga wanda ya so, a lokacin da ya so, kuma wajan sa Lado ke nema.

Injiniya Bishir Sani ya ƙara jinjinawa jama’ar da ke wannan hidima ta lado ba dare ba rana kuma da kuɗaɗen aljihun su suke amfani ba tare da an ba su ko sisi ba.

Daga ƙarshe ya yi ƙira ga jama’a da su tabbatar an zaɓi jam’iyyar PDP daga sama har ƙasa domin fitar da al’umma cikin mawuyacin halin da suke cikin sakamakon fadawa hannun waɗanda ba su iya mulki ba. (Yan sari)

Share

Related

Source: Popular News
Via: Katsina City News
Previous Post

How policeman killed 2 children, injured others over N2,000 bribe in Katsina

Next Post

ƳAN BINDIGA SUN SAKE KAI HARI BATSARI

Next Post
ba mutane 39 aka sace a Katsina ba – Ƴan sanda

ƳAN BINDIGA SUN SAKE KAI HARI BATSARI

Recent Posts

  • APC ta gano kafafen yada labaran da PDP ke ɗaukar nauyi su yaɗa karya a kan Tinubu
  • Emefiele: We’ve collected N1.9trn old naira notes so far — N900bn more to go
  • Hanyoyi Shida Domin Kiyaye Basir Cikin Sauƙi.
  • Bankin CBN Ya Samar Da Naira Miliyan 120 Domin Yin Canjin Kudi A Katsina.
  • INEC ta kara tsawaita wa’adin karbar katin zabe

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In