Gwamnan babban bankin kasar, Godwin Emefiele, ya ce Hadaddiyar Daular Larabawa na barazanar haramta biza saboda kudaden kamfanonin jiragen sama da suka makale a Najeriya.
Mista Emefiele yayin wani zaman tattaunawa da shugaban majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila ya shirya, ya ce bankin na CBN ya saki dala miliyan 110 ga kamfanonin jiragen sama na kasashen waje a watan Agusta kuma zai sake sakin wasu dala miliyan 120 a ranar 31 ga watan Oktoba.
Source:
Katsina City News
Via:
Zaharadeen