• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Asalin fara sanya Karatun Kur’ani a rediyo…

Katsina City News by Katsina City News
March 31, 2023
in Sashen Hausa
0
Asalin fara sanya Karatun Kur’ani a rediyo…
0
SHARES
16
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

A 1951 Gwamnatin mulkin mallaka ta kafa gidan rediyon NBS a Legas tare da rassansa a Ibadan da Inugu da Kaduna. Tun a 1932 dai aka fara sauraron rediyo a Najeriya bisa tsarin RDS, amma baki dayan

shirye-shiryen na Ingilishi ne zalla. Don haka aka kafa NBS saboda a fara gudanar da shirye-shirye a Najeriya kuma cikin harsunan yan kasa. Wannan gidan rediyo na NBS shi ne ya fara saka karatun Alkurani Mai girma a tasharsa da ke Kaduna. Sai dai hakan ya jawo ce-ce- ku-ce. Domin kuwa Musulmi da ke Arewacin Najeriya sun koka da suka ji karatun Kurani a cikin naura ta ‘sharholiya irin rediyo wadda aka saba jin kade-kade da kuma zantuttukan duniya a cikinta. Don haka suka yi ta rubuta wasikun korafi zuwa ga

gidan rediyon inda suka bukaci a daina sa Kur’ani saboda yin hakan tamkar wulakanta shine. Sarkin Kano Muhammadu Sanusi shi ne Shugaban Hukumar Daraktocin Gidan Rediyon a wancan lokaci. Don haka a

wurinsa shugabannin gidan rediyon suka nemi mafita. A 1954 Sarki Sanusi ya dakatar da saka karatun Kurani a rediyo, inda ya nemi fatawa daga malaman Tijaniya na Kano da kuma Sarkin Zazzau Jaafaru dan Isiyaku, wanda shi ne wanda ake gani ya fi kowanne Sarki a Arewacin Najeriya ilimin addini a lokacin. Malaman Kano sai suka aike da fatawar zuwa ga Shehinsu Ibrahim Inyass. Amma sai baki ya rabu biyu. Shehi Inyass ya ba da fatawar cewa

saka karatun Kurani a rediyo ya halatta yayin da Sarkin Zazzau Jaafaru ya ce tunda yake babu wani nassi karara da ya bayyana halacci ko haramcin saka Kurani a rediyo, yana ganin gara kada a sa saboda kada a bude kofar keta alfarmar Littafi mai girma.

Ganin ansamu wannan sabani sai É—aliban Inyass na Kano suka tura masa da Fatawar sarkin Zazzau. Daga nan ya rubuto littafi mai taken “Alhujja al’baligha fi kaunil  Iza’atul Æ™ur’ani Sa’igha. Inda anan ne yayi bayani cikakke tare da kawo gamsassun hujjoji cewa, sa karatun Ƙur’ani a rediyo ko bai kai matsayin wajibi ba, yakai matakin halal abin so. 

Bayan samun wannan Fatawar ce aka ci gaba da saka karatun Alqur’ani a radiyo.

Share

Related

Source: Jaridar Aminiya
Via: Katsina City News
Previous Post

Tuna Baya: Yanda aka fara Tafsir a watan Ramadan 

Next Post

Yanda aka fara sanya Tafsiri a Rediyo.

Next Post
Yanda aka fara sanya Tafsiri a Rediyo.

Yanda aka fara sanya Tafsiri a Rediyo.

Recent Posts

  • Ƙungiyar ‘Yan jarida ta Najeriya za ta fara yajin aiki kan cire tallafin mai
  • Nigeria Loses 965 Soldiers, Policemen To Boko Haram, IPOB In 2 Years
  • Gbajabiamila ya gode wa Tinubu bisa naÉ—a shi shugaban ma’aikata
  • Tinubu ya jajanta wa Indiya kan hatsarin jiragen Æ™asa
  • Hajj 2023: Azman begins airlift of pilgrims Today

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • June 2023
  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.