• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

An gurfanar da Tukur Mamu a gaban kotu

Katsina City News by Katsina City News
March 21, 2023
in Sashen Hausa
0
An gurfanar da Tukur Mamu a gaban kotu
0
SHARES
15
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

An gurfanar da tsohon mai shiga tsakani da ‘yan bindigar da suka sace fasinjojin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna Tukur mamu a gaban kotu, kan zarge-zarge 10 da suke da alaƙa da ɗaukar nauyin ta’addanci.

An dai kama Tukur Mamu ranar 6 ga watan Satumban 2022 a filin jirgin saman birnin Alqahira na ƙasar Masar a kan hanyarsa ta zuwa Saudiyya, inda aka mayar da shi Najeriya.

Gwamantin Najeriya dai na zargin Tukur Mamu da taimaka wa ‘yan Boko Haram wajen shirya tare da ƙaddamar da hare-harensu kan ‘yan ƙasar da ba su ji ba, ba su gani ba..

Ana kuma zarginsa da karɓar maƙudan kuɗaɗe daga hannun iyalan fasinjojin jirgin ƙasan da ƙungiyar Boko Harama ta yi garkuwa da su.

An zarge shi karɓar dala 420,000 da kuma naira miliyan 21 daga hannun iyalan fasinjojin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna.

An kuma zarge shi da ɓoye kuɗin da ake shirya ta’addanci a gidansa na jihar Kaduna da ke arewacin ƙasar

To sai dai Tukur Mamu ya musanta duka zarge-zargen da aka karanto masa a gaban kotun.

Lauyan Tukur Mamu ya nemi da a bayar da belinsa saboda a cewarsa wanda yake karewar na fama da wani rashin lafiya da ke buƙatar tiyatar gaggawa.

To sai dai lauyan gwamnati ya nuna rashin amincewa da belin Mamu, yana mai cewa duk ciwon da ke damun wanda ake zargin ana iya magance shi a asibitin jami’an tsaron DSS inda yake tsare.

Haka kuma bayan doguwar muhawara alƙalin kotun mai shari’a Inyang Ekwo ya ce Tukur Mamu zai ci gaba da kasancewa a hannun jami’an DSS ɗin har zuwa lokacin da za a yanke hukunci kan bukatar belin nasa.

Share

Related

Source: BBC Hausa
Via: Katsina City News
Previous Post

Dan takarar jam’iyar PDP, Kefa ya lashe zaɓen gwamna a Taraba

Next Post

Ganima Ko Amana: Kalubalen Shugabanni! -Mahuta

Next Post
Ganima Ko Amana: Kalubalen Shugabanni!  -Mahuta

Ganima Ko Amana: Kalubalen Shugabanni! -Mahuta

Recent Posts

  • Hajj 2023: Azman begins airlift of pilgrims Today
  • Hajj Airlift: NAHCON Airlift 14,000 pilgrims in 33 flights operations, set up back up plans
  • Hajj 2023: Plateau pilgrims “stranded’ over “failure to remit funds” for Hajj officials
  • Abin da aka tattauna a taron Tinubu da gwamnonin Jam’iyyar APC
  • Makkah service providers pledges ‘memorable’ Hajj 2023 for Nigerian pilgrims

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • June 2023
  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.