• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Monday, January 30, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

AL’AJABI: Ko Kun San Garin Da Mata Ne Kawai Suke Sarauta A Arewacin Nijeriya?

January 4, 2023
in Sashen Hausa
0
AL’AJABI: Ko Kun San Garin Da Mata Ne Kawai Suke Sarauta A Arewacin Nijeriya?
0
SHARES
25
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Shin kun taɓa sanin cewa, akwai wata masarauta da mata zalla ke mulki a arewacin Nijeriya?

Masarautar Dingep da ke Ƙaramar Hukumar Ganye a jihar Adamawa a arewa maso gabashin ƙasar ta shafe sama da ƙarni Bakwai ƙarƙashin jagorancin mata, wani abu da ya sha bambam da sauran masarautu da ke arewacin ƙasar.

Garin ya na da yawan jama’a sama da mutum Ɗari Biyar, kuma sarauniya ce ke gudanar da dukkan aikace-aikace da sarakunan gargajiya maza ke yi a wasu masarautun.

Har kawo wannan ƙarni na Ashirin da Ɗaya (21st century) da ake ganin duniya ta ci gaba da wayewa ta fuskoki da daman gaske, ake kuma ganin akwai sabon salo na rayuwa, kama daga harkar ta fi da mulki zuwa sauran sha’anin rayuwa, a ɓangaren masarautun gargajiya ba a rasa masarautun da suke ƙarƙashin kulawa da ikon mata ba har yanzu.

Tarihi

Ɗaya daga cikin irin waɗannan masarautu dai itace masarautar Arnado Debbo da ke ƙarƙashin masarautar Ganye a jihar Adamawa, in da a tarihin kafuwa da ci gaba da wanzuwar masarautar; Mata ne ke shugabancin masarautar a kuma zauna lafiya.

Kamar yadda masana tarihin masarautar suka bayyana, ba a taɓa samun namiji da ya shugabanci masarautar kuma ya yi tsawon rai ba.

Ma’anar kalmar “Arnado Debbo” da Fulatanci shi ne (Jagorancin Mace) wadda kuma ita ce kalmar da garin ya samo sunansa, a don haka a tarihin tsawon kafuwar garin ya ci gaba da amsa wannan suna sakamakon sarautar da mata ke yi.

Masarautar Arnado Debbo dai, daɗaɗɗiyar masarauta ce mai cike da tarihin gaske, don kuwa ita ce sila da salsalar kafuwar masarautar Ganwari Ganye har ma da samuwar garin Ganye baki ɗaya, kana ta ƙunshi wasu gundumomi da suke ƙarƙashinta da suka haɗa da Dimaeb, Dapellum, Sayikmi, Dauera, Naburapeu, Dimkolum, da Samjerum.

Wani abin mamaki shi ne, kusan kashi 70 bisa 100 na jama’ar masarautar Musulmi ne, wadda ba kasafai ake samun mace ta yi shugabanci a cikinsu ba musamman ma kan sha’anin sarauta.

Daga Taskar Nasaba ( zamani media crew)

Share

Related

Source: Katsina City News
Via: Zamani
Previous Post

Internal Wrangling in Katsina PDP Threatens Atiku, Lado’s Chances

Next Post

Katsina PDP guber candidate flags off campaign, vows to win

Next Post
Katsina PDP guber candidate flags off campaign, vows to win

Katsina PDP guber candidate flags off campaign, vows to win

Recent Posts

  • APC ta gano kafafen yada labaran da PDP ke ɗaukar nauyi su yaɗa karya a kan Tinubu
  • Emefiele: We’ve collected N1.9trn old naira notes so far — N900bn more to go
  • Hanyoyi Shida Domin Kiyaye Basir Cikin Sauƙi.
  • Bankin CBN Ya Samar Da Naira Miliyan 120 Domin Yin Canjin Kudi A Katsina.
  • INEC ta kara tsawaita wa’adin karbar katin zabe

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In