• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Akwai ’Yan Siyasar Da Ke Kokarin Hana Rantsar Da Tinubu – DSS

Katsina City News by Katsina City News
March 29, 2023
in Sashen Hausa
0
Akwai ’Yan Siyasar Da Ke Kokarin Hana Rantsar Da Tinubu – DSS
0
SHARES
31
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

DSS ta gargadi mutanen da su canza shawara ko su kuka da kansu

Hukumar tsaro ta DSS ta ce akwai wasu ’yan siyasa da ke kokarin hana rantsar da zababben Shugaban Kasa, Bola Tinubu, ta hanyar yunkurin kafa gwamnatin rikon kwarya.

A ranar 29 ga watan Mayu mai zuwa ce aka shirya za a rantsar da sabon shugaban, inda zia karbi ragamar kasar daga shugaba mai barin gado, Muhammadu Buhari.

Sai dai a cewar Kakakin hukumar ta DSS, Peter Afunanya, a cikin wata sanarwa da yammacin Laraba, wadanda hukumar take zargi na ta duba hanyoyi da dama, cikinsu har da kokarin samo umarnin kotun da zai hana rantsuwar ta yadda dole za a kafa gwamnatin rikon kwarya.

Afunanya ya kuma ce yanzu haka mutanen na shirye-shiryen daukar nauyin zanga-zanga a manyan biranen Najeriya ta yadda za a ayyana dokar ta-baci.

Sanarwar ta ce, “Hukumar na kallon irin wadannan yunkurin ba wai kawai a matsayin wanda bai dace ba, kazalika kuma yin zagon kasa ne ga Kundin Tsarin Mulki da kuma kokarin jefa kasa cikin rikicin ba gaira ba dalili.

“Wannan ba abu ba ne mai yuwuwa, koma yin karan tsaye ne ga tsarin Dimokuradiyya da kuma ra’ayin ’yan Najeriya masu son zaman lafiya,” in ji sanarwar.

DSS ta kuma ce tana goyon bayan shirye-shiryen mika mulki cikin ruwan sanyi, kuma za ta yi aiki tukuru wajen ganin hakan ta tabbata.

“A kan haka, muna aike wa da kakkarfan sakon gargadi ga irin wadannan mutanen da ke son yi wa Dimokuradiyya a Najeriya zagon kasa da su kuka da kansu kuma su canza shawara tun da wuri.

“Muna kuma kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da suka hada da bangaren shari’a da kafafen yada labarai da kungiyoyin fararen hula da su yi taka-tsantsan wajen kauce wa yin amfani da su wajen kawo wa tsarin zaman lafiya cikas.

“Yayin da za mu ci gaba da sanya idanu, hukumar DSS ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen sanya kafar wando daya ta hanyar daukar matakin doka a kan irin wadannan bata-garin ’yan siyasar marasa kishin kasa,” in ji sanarwar da DSS.

Share

Related

Source: Aminiya
Via: Katsina City News
Previous Post

APC Govs: Tinubu Will Turn Nigeria Around

Next Post

Gawuna Ya Taya Abba Gida-Gida Murnar Lashe Zaben Gwamnan Kano

Next Post
Gawuna Ya Taya Abba Gida-Gida Murnar Lashe Zaben Gwamnan Kano

Gawuna Ya Taya Abba Gida-Gida Murnar Lashe Zaben Gwamnan Kano

Recent Posts

  • Hajj 2023: Azman begins airlift of pilgrims Today
  • Hajj Airlift: NAHCON Airlift 14,000 pilgrims in 33 flights operations, set up back up plans
  • Hajj 2023: Plateau pilgrims “stranded’ over “failure to remit funds” for Hajj officials
  • Abin da aka tattauna a taron Tinubu da gwamnonin Jam’iyyar APC
  • Makkah service providers pledges ‘memorable’ Hajj 2023 for Nigerian pilgrims

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • June 2023
  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.