• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Friday, March 31, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Abin Da Zan Yi Idan Tinubu Ya Ba Ni Mukami A Gwamnatinsa -Peter Obi

March 16, 2023
in Sashen Hausa
0
Abin Da Zan Yi Idan Tinubu Ya Ba Ni Mukami A Gwamnatinsa -Peter Obi
0
SHARES
38
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ya ce ba zai amince da duk wani tayin mukami da gwamnatin Bola Tinubu za ta yi masa ba.

Obi ya maka Tinubu, zababben shugaban kasa da jam’iyyarsa ta APC a gaban kotu kan sakamakon zaben da aka yi a ranar 25 ga watan Fabrairu.

APC ya yi nuni da cewa tsohon Gwamnan Legas zai kafa gwamnatin hadin kai domin tafiyar da dukkan masu adawa da shi a cikin gwamnatinsa.

Yayin da yake magana a talabijin na Channels a ranar Alhamis, Obi an tambaye shi ko me zai yi idan aka kira shi ya zama mamba a gwamnatin Tinubu ta hadin kan kasa.

A martaninsa, Obi ya ce har yanzu yana kalubalantar yadda zaben ya gudana da kuma ayyana Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben.

A cewarsa, kamata ya yi a sanya tsarin zaben yadda ya kamata kafin kowa ya yi maganar gwamnatin hadin kan kasa.

“Abu na farko da nake son gani shi ne tsarin ya yi daidai. Hanyar da kuka cimma wani abu ya fi muhimmanci fiye da abin da kuke yi bayan haka. Ina kalubalantar tsarin.

“Har sai mun daidaita, sannan za mu iya magana game da gwamnatin hadin kan kasa. Idan ba haka ba, sai mu je mu zauna mu ce wadanda suka tare jirgin kasa suka yi garkuwa da mutane za su iya kiranmu mu tattauna batun zaman lafiya idan suna da mutane a tsare. Har sai an yi abubuwa daidai, za mu karfafa abin da ba ma bukatar karfafawa, ”in ji shi.

Da aka tambaye shi ko zai amince da sakamakon, Obi ya ce zai yi mamaki idan kotu ta amince da zaben Tinubu.

“Za a warware batutuwan da suka shafi zaben a kotu. Zan yi mamaki idan kasar nan ta ci gaba a wannan yanayin. Ba za mu iya kyale shi ba. Muna bukatar mu fara kwance wannan laifin.

“Lokacin da mutane ke magana game da tsari, wannan zamba da aka aikata laifi ne kuma mun shaida cewa suna magana akai, kuma muna so su gyara saboda ‘ya’yanmu.”

Tsohon gwamnan Jihar Anambra, ya ce ya yi imanin bangaren shari’a za su yi abin da ya dace.

Share

Related

Source: Leadership Hausa
Via: Katsina City News
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Cire Tallafin Man Fetur Kafin 29 Ga Watan Mayu

Next Post

Jihohin da ba za a yi zaɓen gwamna ba a ranar Asabar

Next Post
Jihohin da ba za a yi zaɓen gwamna ba a ranar Asabar

Jihohin da ba za a yi zaɓen gwamna ba a ranar Asabar

Recent Posts

  • On birthday, clerics pray for Tinubu, Nigeria in Abuja
  • Gwamna Masari ya Kaddamar da Kwamitin Miƙa Mulki ga sabuwar Gwamnati
  • Masari: Tinubu Na Bukatar Addu’a
  • Bashin Da Ake Bin Najeriya Ya Karu Zuwa N46.25tr —DMO
  • FEC Approves N59.78bn For Ogoni Cleanup Projects

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In