• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Monday, January 30, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

2023: Kotu ta tabbatar da hukuncin korar Al-Mustpha da wasu ƴan takarar AA

December 22, 2022
in Sashen Hausa
0
2023: Kotu ta tabbatar da hukuncin korar Al-Mustpha da wasu ƴan takarar AA
0
SHARES
16
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

A yau Alhamis ne wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da bukatar ta janye hukuncin da ta yanke a ranar 4 ga watan Nuwamba na amincewa da ‘yan takarar da jagorancin Dr Adekunle Rufa’i Omo-Aje ya jagoranta na jam’iyyar Action Alliance (AA).

Mai shari’a Zainab Abubakar, a hukuncin da ta yanke, ta ce karar da Kenneth Obidiche Udeze ke jagoranta ya shigar ba ta da wani inganci.

Kamfanin dillancin labarai na Ƙasa ya rawaito cewa mai shari’a Abubakar a ranar 4 ga watan Nuwamba ta umarci hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) da ta amince da ƴan takarar da jagorancin Omo-Aje na jam’iyyar AA ya gabatar domin zaɓen 2023.

Alkaliyar ta kuma umurci INEC da ta yi watsi da ‘yan takarar da shugabancin ɓangaren Udeze ya gabatar, daga cikinsu har da Manjo Hamzat Al-Mustpha (mai ritaya).

Amma Udeze, wanda aka amince da dakatarwarsa da kuma korar shi a matsayin shugaban AA na kasa a wasu hukunce-hukunce guda biyu na kotun daukaka kara, ya bukaci babbar kotun ta Abuja da ta janye hukuncin na ranar 4 ga watan Nuwamba, yana mai cewa an same shi ta hanyar zamba ne, kuma ya na da’awar cewa har yanzu shi ne shugaban jam’iyyar na kasa.

Da ta ke yanke hukuncin a yau, Mai shari’a Abubakar, ta ce, bayan hukuncin kotun daukaka kara biyu da kuma wani hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke a Abeokuta, Udeze ba zai iya yin ikirarin cewa shi ne shugaban jam’iyyar ba a bisa doka.

Hukunce-hukunce guda biyu na Kotun Daukaka Kara an yanke su ne a ranar 7 ga watan Janairu da 11 ga watan Nuwamba, yayin da kotun Abeokuta ta yanke hukuncin a ranar 8 ga watan Satumba, ƙarƙashin mai shari’a J. O. Abdulmalik a cikin wata kara mai lamba: FHC/AB/CS/120/2022.

Alkalin kotun ta ce hukuncin da ta yanke a ranar 4 ga watan Nuwamba bai samu ta hanyar zamba ba kamar yadda Udeze ya yi zargi.

Ta bayyana Udeze a matsayin mutum ne mai cike da ruɗani kuma mai shiga tsakani, ya na kokarin tsoma baki a harkokin jam’iyyar da aka dakatar da shi daga bisani kuma aka kore shi.

Don haka Abubakar ta yi watsi da karar.

NAN ta ruwaito cewa Al-Mustapha, tsohon mai taimaka wa marigayi Janar Sani Abacha ne ya lashe zaben fidda gwanin takarar shugaban kasa na jam’iyyar da bangaren Udeze suka gudanar da jimillar kuri’u 506, inda ya doke Samson Odupitan wanda shi ne abokin hamayyarsa tilo a ranar 9 ga watan Yuni a Abuja.

Share

Related

Source: Daily Nigerian Hausa
Via: Katsina City News
Previous Post

Gwamnan Babban Bankin Najeriya Godwin Emefiele Ya Sake Kin Amsa Gayyatar Majalisar Wakilai

Next Post

Gamayyar Kungiyar Support Groups a ƙarƙashin Dakta Baffa Babba Ɗan’agundi ta ziyarci Katsina.

Next Post
Gamayyar Kungiyar Support Groups a ƙarƙashin Dakta Baffa Babba Ɗan’agundi ta ziyarci Katsina.

Gamayyar Kungiyar Support Groups a ƙarƙashin Dakta Baffa Babba Ɗan'agundi ta ziyarci Katsina.

Recent Posts

  • APC ta gano kafafen yada labaran da PDP ke ɗaukar nauyi su yaɗa karya a kan Tinubu
  • Emefiele: We’ve collected N1.9trn old naira notes so far — N900bn more to go
  • Hanyoyi Shida Domin Kiyaye Basir Cikin Sauƙi.
  • Bankin CBN Ya Samar Da Naira Miliyan 120 Domin Yin Canjin Kudi A Katsina.
  • INEC ta kara tsawaita wa’adin karbar katin zabe

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In