• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

Ƙungiyar Marubuta ta Alƙalam Za Ta Yi Taron Tunawa Da Marubuci Marigayi Mahmoon Baba-Ahmed

Katsina City News by Katsina City News
February 2, 2023
in Sashen Hausa
0
Ƙungiyar Marubuta ta Alƙalam Za Ta Yi Taron Tunawa Da Marubuci Marigayi Mahmoon Baba-Ahmed
0
SHARES
9
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

PRESS RELEASE

Ƙungiyar Marubuta ta Alƙalam Za Ta Yi Taron Tunawa Da Marubuci Marigayi Mahmoon Baba-Ahmed

Ƙungiyar Marubuta Alƙalam da ke Kaduna ta bayyana cewa za ta shirya taron tunawa da uban ƙungiyar kuma gwarzon ɗan kishin ƙasa ɗin nan, Alhaji Mahmoon Baba-Ahmed, wanda Allah ya yi wa rasuwa shekaru biyar da su ka gabata.

Shugabar ƙungiyar, Hajiya Halima Abdullahi K/Mashi, ta bayyana a cikin wata takarda ga manema labarai cewa za a yi taron a Gidan Arewa da ke Kaduna a ranar Alhamis, 9 ga Fabrairu, 2023, wadda ta yi daidai da shekaru biyar cur da rasuwar marubucin.

Alhaji Mahmoon ya rasu ne a Kaduna a ranar Alhamis, 9 ga Fabrairu, 2018, ya na da shekaru 77 a duniya.

Mahmoon Baba-Ahmed sanannen ɗan jarida ne kuma marubuci wanda ya yi fice a aikin rediyo a matsayin wakilin gidan Rediyon Nijeriya na Kaduna a jihohi da dama. Daga bisani ya riƙe muƙamai da su ka haɗa da Shugaban gidan Rediyon Kano da Manajan Daraktan Hukumar Yaɗa Labarai ta Jihar Kaduna (KSMC).

Haka kuma ya kasance mai sharhi kan al’amurran yau da kullum a filayen musamman da aka ware masa a jaridu da su ka haɗa da Triumph, Blueprint da Aminiya, da kuma gidajen talabijin na DITV da Liberty da gidan rediyo na Alheri da na Liberty.

Marigayi Mahmoon ya rubuta littattafan adabi guda shida a rayuwar sa waɗanda su ka haɗa da littafin waƙe mai suna ‘Ɗan Hausa’, da littattafan wasan kwaikwayo guda biyu (‘Uwani Reza’ da ”Yar Halas’), da fassarar littattafai uku na mashahurin marubucin nan na ƙasar Ingila, wato William Shakespeare.

Littattafan Shakespeare da ya fassara su ne: ‘Macbeth’ (‘Makau’), ‘Julius Caesar’ (‘Jarmai Ziza’), da ‘Romeo and Juliet’ (‘Habiba Ta Habibu’).

Takardar sanarwar ta ce ɗaya daga cikin abubuwan ban-sha’awa da za a gudanar a taron shi ne gabatar da littafin ƙarshe da Mahmoon ya rubuta, wato ‘Habiba Ta Habibu’, wanda shi kaɗai ne marigayin bai samu bugawa ba har ya rasu, amma an buga shi a bana.

Hajiya Halima ta kuma bayyana cewa Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, shi ne babban baƙo na musamman a taron, yayin da Shugaban gidan talabijin da rediyo na Liberty, Dakta Ahmed Tijjani Ramalan, shi ne shugaban taron.

Bugu da ƙari, Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli, zai kasance uban taron, yayin da tsohon Shugaban Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Tarayya, Mai Shari’a Umaru Abdullahi (Walin Hausa), shi ne babban baƙo na musamman.

Ta ce Shugaban Shiyyar Kaduna ta hukumar Gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN), Alhaji Buhari Auwalu, shi ne babban baƙo mai jawabi, sannan babban malami a Jami’ar Ahmadu Bello, Farfesa Adamu Ibrahim Malumfashi, zai yi sharhi kan littattafan marigayin.

A cewar shugabar ƙungiyar, manufar taron ita ce a tuno da muhimman ayyukan kishin ƙasa da Alhaji Mahmoon yayi, tare da ƙara kwaɗaita wa jama’a muhimmancin sambarka ga magabatan mu da su ka ba da gudunmawa ga cigaban ƙasa ta hanyoyin da Allah hore masu.

Ta ce za kuma a yi amfani da wannan damar a karrama wasu ‘ya’yan ƙungiyar ta Alƙalam waɗanda su ka riga mu gidan gaskiya.


Sa hannu:

Hajiya Halima Abdullahi K/Mashi
Shugaba
Ƙungiyar Marubuta Alƙalam
Kaduna
1 ga Fabrairu, 2023

Share

Related

Source: Katsina City News
Via: Katsina City News
Previous Post

Alkalam Writers to hold public commemoration, book presentation on late broadcaster, author Mahmoon Baba-Ahmed

Next Post

Gwamna Masari Ya Yi Gaisuwar Ta’aziyyar Ga Gwamnan Nasarawa.

Next Post
Gwamna Masari Ya Yi Gaisuwar Ta’aziyyar Ga Gwamnan Nasarawa.

Gwamna Masari Ya Yi Gaisuwar Ta'aziyyar Ga Gwamnan Nasarawa.

Recent Posts

  • Hajj 2023: Azman begins airlift of pilgrims Today
  • Hajj Airlift: NAHCON Airlift 14,000 pilgrims in 33 flights operations, set up back up plans
  • Hajj 2023: Plateau pilgrims “stranded’ over “failure to remit funds” for Hajj officials
  • Abin da aka tattauna a taron Tinubu da gwamnonin Jam’iyyar APC
  • Makkah service providers pledges ‘memorable’ Hajj 2023 for Nigerian pilgrims

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • June 2023
  • May 2023
  • April 2023
  • March 2023
  • February 2023
  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • English
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Interview
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Press Release
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Sashin Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.