• About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact
Monday, January 30, 2023
  • Login
Katsina City News
Advertisement
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta
No Result
View All Result
Katsina City News
No Result
View All Result
Home Sashen Hausa

“Ƙasar da babu ranar da zata zo ba a kashe mutum ba, nan ne wasu ke amsar kudi su zaɓo mana ɓata gari” Cmr. Bishir Dauda

November 27, 2022
in Sashen Hausa
0
“Ƙasar da babu ranar da zata zo ba a kashe mutum ba, nan ne wasu ke amsar kudi su zaɓo mana ɓata gari” Cmr. Bishir Dauda
0
SHARES
10
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Kungiyar “Citizens Participation Agains Curraption Initiative” ta shirya zama na musamman da kungiyoyin Matasa don kaucewa Rikicin Zaɓe

Kungiyar ƙarƙashin jagorancin Dan Gwagwarmaya Comrade Bishir Dauda ta shirya taron a Sakatariyar Kungiyar ‘Yanjaridu ta ƙasa reshin jihar Katsina a ranar Asabar, inda ta gayyaci kungiyoyin Matasa, da masu ruwa da tsaki akan shirya zaɓe da wayar da kai, Irin su Hukumar gyara ɗabu’a ta ƙasa NOA, da Hukumar INEC, da Kungiyar ‘Yanjaridu ta ƙasa reshen jihar Katsina NUJ.

Da yake bayyana maƙasudin taron Comrade Bishir Dauda ya bayyana dalilin wannan haɗuwa da wakilan ƙungiyoyi daban-daban domin haɗuwa a tattauna yanda za’a iya wayar da kan al’umma domin kaucewa rikicin zaɓuka masu zuwa, da kaucewa shiga bangar Siyasa.

Comrade ya bayyana ire-iren Aikace-aikace da ƙungiyar take da kuma wanda zata tunkara a nan gaba, yace musamman sanya ido a kalaman ‘Yan Siyasa wanda zasu iya tada zaune tsaye, yace kungiyar a shirye take da ta binciki tare da kai ƙarar duk wani ɗan Siyasa da yake kalaman ɓatanci da zasu iya jawowa ƙasa rashin zama lafiya. Da yake jawabi a wajen taron tsohon Darakta a hukumar gyaran aƙida ta ƙasa NOA, Comrade Yusha’u Mani ya ja hankalin matasa akan kaucewa ɓarna da ɗora rayuwar su bisa turbar da ta dace, yace “Mu da kuke gani masu yawan shekaru zamu iya cewa tamu ta ƙare mun yi karatu kyauta, munyi aikin gwamnati kuma mun gama, ku yanzu kune zaku gina gobenku.” Yace abin bakinci shine, yau tsaffin da suka mori ƙasar nan suka samu ilimi da rayuwa mai inganci, sune yau suke jafa matasa cikin halin laha’ula,i.” Comrade Mani ya yi kira ga malamai da suji tsoron Allah, su daina hawa mimbari suna amfani da Addini domin yaɗa fitina cikin Siyasa, yace siyasa ba Addinin bace, adaina amfani da Addini wajen wawaitar da hankalin mutane a Siyasa.

Shima da yake tsokaci a wajen taron wakilin hukumar zaɓe ta INEC a jihar Katsina, PRO na hukumar ya bayyana kokarin da suke na ganin an yi zaɓe cikin kwanciyar hankali da tabbatar wa Al’umma cewa yanda suka shirya zaɓen bisa adalci, da tsari, babu batun maguɗi a cikinsa, yace shiyasa ma wasu ke tsoron Na’urar zaɓen saboda suna ganin ba zata yi masu abinda suke so ba. Sannan yasha alwashin cewa zaɓe ne na gaskiya kuma ko wanene yaci zaɓe za’a tabbatar masa da zaɓensa.

Da yake Magana shugaban NUJ na jihar Katsina da ya samu wakilcin Comrade Aminu Musa Bukar, ya bayyana Illolin rashin zama lafiya a cikin al’umma, yace “Mu ‘Yanjarida muke da rauwar da zamu taka wajen fadakar da mutane, illar hakan.” Yace idan babu zama lafiya ko nan wajen taron ma ba zamu iya zuwa ba, don haka zama lafiya shine farko kafin komai.

Shugabannin kungiyoyin farar hula daban-daban ne suka halarta kuma suka tofa albarkacin bakinsu, gami da kira ga wannan ƙungiya da kada ta gajiya taci gaba da irin wannan tarurruka domin wayar da kai.

Daga cikin bakin da suka halarci taron akwai Bashir Dauda, Aminu Musa Bukar, Comrade Salisu Hafijo, comrade Hamza Umar Saulawa, Comrade Muntari Lawal Tsagem, Comrade Nura Siniya ‘Yan jaridu da sauran kungiyoyin.

Share

Related

Source: Katsina City News
Via: Katsina City News
Previous Post

Gwamnatin Kano ta rufe kamfanin sarrafa ƙarafa na ƴan China bisa karya dokar tsafta

Next Post

Anyaoku, Kukah, Omoigui Okauru, Falola praise Musikilu Mojeed’s The Letterman

Next Post
Anyaoku, Kukah, Omoigui Okauru, Falola praise Musikilu Mojeed’s The Letterman

Anyaoku, Kukah, Omoigui Okauru, Falola praise Musikilu Mojeed's The Letterman

Recent Posts

  • APC ta gano kafafen yada labaran da PDP ke ɗaukar nauyi su yaɗa karya a kan Tinubu
  • Emefiele: We’ve collected N1.9trn old naira notes so far — N900bn more to go
  • Hanyoyi Shida Domin Kiyaye Basir Cikin Sauƙi.
  • Bankin CBN Ya Samar Da Naira Miliyan 120 Domin Yin Canjin Kudi A Katsina.
  • INEC ta kara tsawaita wa’adin karbar katin zabe

Recent Comments

No comments to show.

Archives

  • January 2023
  • December 2022
  • November 2022
  • October 2022
  • September 2022
  • August 2022
  • July 2022

Categories

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina

Browse by Category

  • Biography
  • City News
  • Condolence
  • Fasahar zamani
  • Featured
  • General Stories
  • History
  • Kula da Lafiya
  • Labaran Fim
  • Literature
  • News and Analysis
  • News and Reports
  • Photo News
  • Rubutu da Marubuta
  • Sashen Hausa
  • Tarihin Kasar Katsina
  • About us
  • Advertise
  • Privacy Policy
  • Contact

No Result
View All Result
  • Home
  • News and Analysis
  • Biography
  • History
  • Photo News
  • Featured
  • Literature
  • Sashen Hausa
  • Weekly Columns
    • Allo
    • Fasahar Zamani
    • Kula da Lafiya
    • Labarun Fim
    • Rubutu da Marubuta

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In