An tashi wasa babu ci tsakanin Super Eagles na Najeriya da kuma ƴan wasan ƙasar Saliyo a wasan neman gurbin gasar cin kofin Afirka.
A karawa ta farko a birnin Benin na Najeriya ƙasashen sun tashi ne 4-4.
Sai da Najeriya ta ci 4-0 daga baya Saliyo ta farke kwallayen.
Najeriya ce ta jagoranci rukuninsu da maki 8, a wasanni huɗu da ta buga.