Hukumar kula da harkokin wutar lantarki a Najeriya ta Nigerian Electricity Regulatory Commission (NERC) ta ce ƙarin kuɗin wutar da ta yi bai shafi waɗanda ke shan wutar a matakin D da E ba.
Waɗanda ke kan kan layin na D da E na samun lantarki ne ta ƙasa da awa 12 a kowace rana kuma hukumar ta ce ƙarin na kashi 50 cikin 100 bai shafe su ba.
Hukumar ta yi ƙarin bayanin ne a matsayin martani ga rahoton da kafafen yaɗa labarai suka ruwaito cewa ƙarin zai shafi kowa da kowa, saɓanin wanda ta yi a watan Nuwamban 2020, inda aka kasa biyan kuɗin gida-gida.
Cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Twitter, NERC ta ce har yanzu na waɗanda ke kan matakin D da E za su ci gaba da samun rahusa tun bayan ƙarin da ta yi.
Sai dai a yanzu an ƙara naira biyu kan kowane KW guda ɗaya, inda waɗanda ke kan matakin A da B da C